Showing 93001 words to 96000 words out of 146738 words
Chapter 32 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt
ranar asabar aka yanke hukunci yi mata tiyata dan abin yaki karewa.
Kanwarta a rikice tazo asibitin dan labari ya kai mata, kuka kamar ranta zai fita, haka aka shiga da ita tiyata tana rike da hannun kanwarta.
A dakin tiyata ana zaro 'ya'yan nan biyu ana kokarin yi mata dinki tace ga garinku nan.
Tashin hankalin da suka fuskanta a asibitin nan ba'a magana.
Kowa ka gani hankalinsa a tashe yake, haka duk sanda aka kalli jariran nan biyu sai an zubar musu da hawaye.
Haka aka kaita gidanta, Taura kamar zaiyi hauka, dauriya kawai yakeyi ba magana, dan inya tuno da jariran yaran nan wadanda ko ganinta basuyi ba sai aji hankalinsa ya tashi.
Kanwarta ita ke kula dasu dan ko gidanta bata koma ba, dayake mijinta shima na gida ne, a karshen layin ma ya kama gida.
Jin ance ta koma gidanta yasa tace itakam dasu zata tafi, duk yanda akaso ta hakura amma taki, kuka ma tasa tace itakam abarta dan bazata iya barinsu ba.
Haka aka hakura ta tafi dasu, sai Taura ya hadata da kanwarsa wacce take shekara 14 suka tafi tana taimaka mata.
Gaba daya Taura ya canza, kullum sai yaje ganin yaran nan hankalinsa ke kwanciya, kowa ya gansu bazai taba cewa basuda uwa ba dan sosai take kula dasu, kowa jinjina mata yakeyi dan yarinyace sannan ko haihuwar fari batai ba.
Duk wani bukatunsu Taura ya dauke musu, sannan ya kasa komawa ma gun aikinsa.
Har yaran nan suka shiga shekara guda, suka fara tafiya, kowa ya gansu abin sha'awa."
Hassan yai ajiyar zuciya yace "A wata rana mahaifinta da mijinta sunyi tafiya sukai hatsari wanda ya dauki rayuwarsu.
Taga tashin hankali ga mutuwar miji ga kula da yara biyu, sannan gashi batasan tanada karamin ciki ba.
Gashi duk yanda akai yaran nan su barta taji da abinda ke damunta sunki dan su itace mahaifiyarsu ita kadai suka sani.
Ita ma ta nemi a barsu, haka ta sha wahalar wannan lokaci duk ta rame ta fige.
Taura tsananin tausayinta yasa ya umarci dauke yaran sai dai kuka tasa ta nemi a barmata wai mijinta ya tafi kar a rabata da 'ya'yanta.
Haka ya bar mata su, har Allah ya kawo mata nata haihuwar ta haifi danta namiji aka sa mai Sageer."
Ajiyar zuciya yai yace "Kin fahimci labari na kashe na farko?"
Jalila wacce idanunta ke zubar da hawaye tace "Kune yaran kanana, sannan wacce ta rikeku wato kanwar mahaifiyarku Ummy ce???"
Hassan yace "eh, Ummy ce."
Haka muka taso mu uku, sai dai nu biyu mun girmi Sageer da shekara biyu, dangin mahaifinsa suka daukeshi saboda takaicin yanda take kula damu.
Haka muna kuka aka tafi dashi, bayan mun dawo gidan mahaifanta ne aka yanke shawarar hada auransu.
Da harta ki amincewa sai dai ganin za'a kwacemu yasa ta amince.
Tunda take bata taba nuna tanasan akawo mata danta ba, duk kuwa da kowa yasan zuciyar uwa.
Haka Abba ya daukemu muka koma Egypt, zamansu zama ne na kara bawai na aurataya ba, har a hankali suka fahimci mahimmancin junansu.
Shekararmu takwas a garin muka dawo nigera, na taso da tsananin kaunar Ummy wanda ko hawaye ko damuwa naga tanayi sai na yi tayin kuka, ganin yanda take zama tai shiru wani sa'in tana kallan hoton Sageer yasa nai ta kuka nace a dawo Nigeria adauko mana shi.
Tundaga lokacin Ummy ta ajiye hoton ta daina daukowa, shima Abba ganin haka yasa ya ajiye aikinsa muka dawo.
Husain nada magana sannan akwai saukin kai, muna tsananin san Ummy sai dai shakuwar dake tsakanina da ita daban ce.
Muna dawowa nace Abba na yaje ya dauko Sageer.
Haka mukaje suka hanamu, gashi a kauye suke sun tubure akan dansu bazaiyi agola ba.
Sai da Abba ya daukeni mukai zuwa kauyen nan sau kusan goma kafin su amince.
Haka suka bamu shi muka kawoma Ummy shi, tayi kuka sosai dan bata taba tunanin za'a bata shi ba.
A kuma lokacin ta dauki alkawarin bazata taba banbantamu da Sageer ba."
Cikin tsananin mamaki Jalila ke jin wannan labarin, to meyasa Uncle yace bazai ko dan abinda su Hassan suka mai bazai iya musu butulci ba? Saboda daukoshi da sukai?
Hassan yai shiru kafin ya dan runtse idanunsa, wani abu na ratsashi.........
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*53*
Wata irin muguwar shakuwa ce tsakanina da Ummy wanda ko mahaifina banajin kaunarsa haka a raina, ita kanta ko yaya naji ciwo kafin nace da zafi fuskarta ce zata nuna tanajin zafin abin, hakan yasa ko banida lafiya banfiya nuna mata ba, Husain nada kawaici sannan baifiya makon uwa kamar ni ba, da farko bamu taba sanin ba Ummy bace ta haifemu saboda yanda muke, har saida muka dawo daga Cairo, mu kawai mun dauka kanin mu Sageer ne kawai babansa daban.
Sageer shikansa baisani ba shi sai da yaje ziyara gun dangin mahaifinsa, sai dai koda wasa bai taba nuna mata ma ya sani ba, duk wani tunani da zakiyi akan yanda Uwa zataso danta Ummy na mana wannan san, Aunty Nana itace yayarsu Ummy amma mahaifiyarta daban, halayenta ba irin na Ummy bane sai dai itama ko da wasa bata nuna mudin ba 'ya'yan Ummy bane, har yau babu wanda na taba ji yace mu ba 'ya'yanta bane sai wanda ya sani tun fil'azal.
Yai shiru sautin numfashinsa ya canza kafin yace "haka rayuwarmu ta taso cikin farinciki da kaunar juna har zuwa shekara 13, a lokacin mu muna shekara sha uku shi kuma Sageer na shekara 11, wannan lokacin ma aka kara samun matsala dan 'yan Uwan mahaifinsa daga zuwansa hutu suka rikeshi wai sun kula Ummy ba ta kawoshi duk hutu da alama so take ta daukeshi.
Hankalinmu ya tashi dan ni da Husain har zazzabi mukai, sai dai ganin Ummy ta watsar da komai yasa muka ware muma.
A wata rana wacce ta zamarmin ranar bakinciki a tarihin rayuwata, a lokacin kanin Abba yazo shida matarsa da 'ya'yansa sunzo gida tayamu murna na suna dan Allah ya albarkaci Ummy da samun 'ya mace ya wato Ameera.
Dukansu mata ne sai Sudais kadai wanda yake namiji sannan shine karami dan shekararshi shida a lokacin, yan uwa da dama sunzo tayamu murna.
Da yake ni duk inda taro yai yawa ba sanshi nake ba hakan yasa na fito daga cikin gida.
Har nayi waje Husain ya kwallamin kira na juyo, yace "ina zaka?"
Dayake akwai shaguna a karshen layin mu nace shago zani, yace "bari inzo muje."
Nan ya taho da sauri, muna fita kofar gida mukaga Sudais, nace "Sudais daga ina?"
Yace "alawa na siyo."
Ya nuna mana alawar hannunsa, Husain ya amshi daya ya bude muka taho mu uku, muna tafe munata hira wanda ni kaina a yanzu na manta hira me mukeyi.
Har mukaje karshen layin, hango wasu maza mukai a kan titi suna kan doki gashi mutane sai kallansu akeyi, abinka da yarinta kawai sai muka kutsa ciki kuna kallo.
Daga tsallaken titi na hango wata mota kamar ta Abba, nace "Husain kaga motar Abba." Ni a guna nasan ba motar bace zolayarsa nakeyi, shikuma yana gani ya yarda yace "ai kuwa muje."
Nace ka bari su gama wucewa.
Nan muka tsaya har suka wuce nace to mu tsallaka, Sudais sai tsalle yake wai ya hango Abba, wanda ni a guna mugunta na shirya inata dariyar yarinta.
Kamar zamu tsallaka titin, harna fara tafiya dasu na dawo baya ina dariya, ina cewa ba Abba bane ziraku nayi.
Husain na rike da hannun Sudais ya juyo shima yana dariya yace "amma lalai Hassan, wallahi ni harna yarda
Shikuma Sudais, duk ya damu a karasa karshen titi, Husain ya kamo hannunsa suka juyo da shirin dawowa.
Gaba daya bamuyi auni ba ina kallansa shima yana kallona muna dariya sai gani nai anyi gaba da..........
Numfashinsa ne ya sarke, wasu zafaffan hawaye ne suke zubomai, karar faduwarsu kawai mukaji.
Sam bamu kula da tahowar mota ba, mutanene suka taho gun a rikice, jini....... jini.......
Numfashinsa ne ya shiga fita da sauri da sauri. Kansa na wani irin sarawa, yace " Tsoro da fargabar abinda na gani na fara ja da baya da baya, ina kallan jinin da ke zuba daga kansu.
Inaji mai motar na tambayar waye ya sansu amma bakina ya kasa magana saboda numfashina da yake hawa da sauka, kaina na wani irin juyawa saboda jinin dake kwaranya.......
Kansa ya matse da karfi wanda ke mai wani irin azaba, Jalila kam hawaye duk ya gama jika mata fuska.
Matsowa tai tasa hannunta akan kafadarsa tace "Yaya?"
Hannunta ya dan ture tunda ya fara labarin sai yanzu ya juyo ya kalleta fuskarsa gaba daya ta canza, bata taba ganin Hassan haka ba, yace "Nine sanadiyar rasa rayukansu, wanda haryau kanin Abba Allah bai kara bashi haihuwa ba, wanda ranar sunan Ameera ya zama ranar rasuwar yayana, wanda nai sanadiyar mutuwar daya daga cikin farin ciki Ummy, farincikin mahaifina sannan farinciki na, bancigaba da makaranta ba saboda na dade a asibiti a kwance, sai dana samu sauki ne Abba ya kawo wani gida yana koyamin, a haka da kyar Ummy ta sani nai exam din waec daga nan ban cigaba da komai ba.
Nine sanadi, Taya zan samu farinciki a rayuwata? Taya zanyi murmushi a rayuwata, tunda abin nan ya faru har yau basusan nine sanadi ba, sai dai kowa tausayamun yake akan rashin dan uwa nane yasa ni canzawa haka? Na lalata farincikin kowa na lalata.......:"
Kansa ya kifa akan sityarin mota yanajin wani abu na ratsashi.
Ya dade a haka kafin yace " ki shiga gun mahaifiyarki, bancancanci samunki ba, bancancanci samun farinciki ba."
Shiru tai tana kallansa sai hawaye dake zubo mata wanda kamar korosu akeyi, hannu tasa ta bude kofar motar ta fita.
Idanunsa ya runtse da karfi yasan za'ai hakab sai dai zuciyarshi ce ta sake zafi dayaji ta fita, hakan shine daidai shikuma yanzu rayuwarsa sai tafi tada dan ta riga ta shiga rayuwarsa wanda yanzu ya tabbatar cireta babbar gibe ne a gareshi.
Jiyai ta sake bude motar, dagowa yai ya hade rai sannan ya kalleta.
Yanzu kam gaban mota ta bude gefensa ta bude, kallanta yai sai dai baice komai ba, Jalila ta shiga ta zauna sannan ta rufe motar, kallansa itama tai sannan tace " Inyi magana?"
Kallansa yai kallan mamaki, tace "ka fadi duk abinda ke ranka ni baka barni na fadi nawa ba."
Yace "kamar ya kenan?"
Shiru tai kafin tace " yaya kana tunanin dan Uwanka abinda yakeso kenan?"
Kallan tambaya ya mata, tace "yanzu in yasan saboda shi ka maida rayuwarka haka kana tunani zaiyi alfahari da hakan?"
Idanu ya kura mata, tace "yaya kana yaro lokacin sannan ba da saninka bane......."
Da sauri ya juya kai ya bude kofa yana neman fita, da sauri tasa hannu ta riko hannunsa.
Juyowa yai ya kalleta tace "inhar kanasan in tafi zan tafi, sai dai inhar akan dalilan nan ne hujjajun basu karbu ba."
Kallanta yakeyi, murmushi tamai tace "wace irinn rayuwa kai zuciyarka na dauke da abubuwan nan?....."
Batai auni ba ya jawo hannunta ta fada jikinsa, kankameta yai tsam, yanajin wani abu na ratsashi, duk da gabanta dake faduwa a hankali tace " meyasa kake tunanin su Ummy zasu ga laifinka akan abinda ya faru?"
Idanunsa ya lumshe kawai, bayansa tadan shafa alamar lalashi tace "Yaya kaine abin tausayi ba su Husain ba, su kansu na tabbatar da zasusan abinda ka aikatawa kanka bazasuji dadi ba."
A hankali ya dagota daga jikinsa kallanta yai, ita kanta kallansa takeyi, sai dai ganin kallan da yake mata yasa ta saukar da idanunta kasa, ya rike fuskarta da hannayensa yace "Jalila kinfi kowa sanin halina, inada dizgi? Shariya? Rashin san magana? Rashin iya magana? Rashin iya hulda da mutane? Kin tabbatar zaki iya zama zama dani?"
Shiru tai tana kallansa, sai dai a wannan lokacin ta tabbatar bazata iya bijire masa ba, batada tabbas akan ko tana sanshi sai dai bazata iya musa mai ba, kai ta daga a hankali.
Kansa ya sunkuyo a hankali saitin bakinta, yakai labbansa kan nata.
Labanta ya tsotsa kadan sannan ya dago ya kalleta yace " banasan na zama nine sanadiyar ruguzamiki rayuwa."
Idanunta ta lumshe dan wani abu taji yana ratsata, a hankali ya kara kai bakinsa cikin nata, wani salo yake mata wanda yasa taji gaba daya kanta na juyawa, wani abu na ratsata har cikin kanta.
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔️ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
Trauma is defined by the American Psychological Association (APA) as the emotional response someone has to an extremely negative event. While trauma is a normal reaction to a horrible event, the effects can be so severe that they interfere with an individual's ability to live a normal life. In a case such as this, help may be needed to treat the stress and dysfunction caused by the traumatic event and to restore the individual to a state of emotional well-being.
Some common sources of trauma include:
Rape
Domestic violence
Natural disasters
Severe illness or injury
The death of a loved one
Witnessing an act of violence e.t.c.
Idan muka duba abinda ke rubuce a sama, zai bamu damar cikaken fahimtar matsalar Hassan, Trauma na ganin mutuwar kaninsa da yake tsananin so sannan da Guilty na laifin da yake tunanin shine sanadiyar yin hakan, kafin na fara rubuta matsalolin Hassan sai danai bincike akan matsalar cutar Trauma wanda ke damunsa, na dauko bayanin sama ne saboda mu fahimci matsalarsa musan me ake nufi da wannan kalma ta Trauma, akwai mutane dayawa dake dauke da wannan matsalar sai dai bama damuwa da abinda ke damunsh saboda rashin sanin matsalarsu, wasu cikin bacci zakaga suna razana, wasu kansu ke daukar zafi, wasu duk sanda sukaga jini, duk wadannan na faruwa ne a yayin da sukai karo da wani mumunan abu wanda ya taba ayuwarsu yakan hanasu yin rayuwa yanda ya kamata.
Allah ya mana mai kyau ameen.....
*54*
A hankali ya dago ya kalleta, itama ta bude idanunta.
Kallansa tai sannan tai saurin saukar da idanunta kasa, ta zame daga jikinsa ta koma ta zauna akan kujera, karamin gyaran murya yai na burin kunya yace " zaki shiga ku gaisa da Goggo?"
Bata kalleshi ba tace "a'a."
Tada mota yai sukai gaba, shiru ne ya ratsa motar ba wanda ya sake magana.
Sunyi tafiya sosai, kafin ta daure tace " Yaushe kuma Ya Sageer din ya dawo?"
Yace "Sageer? Bayan abin ya faru ne hankalin su Abba ya tashi shine suka nemi alfarma akan a dawo dashi, ko hankalina dana Ummy zai kwanta, dakyar dai suka amince."
Ta dan kalleshi tace " Yaya na kasa fahimtar abu daya, me yasa kafi damuwa da Ummy kadai? Dan na kula yanda ka damu da Ummy baka damu da Abba ba."
Kallanta yai sannan yace "haka kike gani?"
Tace "bani kadai ba hakan ne ma."
Shiru yai har kamar bazaiyi magana ba sai yace " Abba a koda yaushe in na ganshi nakanji tsananin tausayinsa, nine sillar rasa dansa da kuma dan kaninsa sai dai yanda yake nunamin so shine ke damuna, i have to be cold to him saboda ya rage damuwa dani, dan ban cancanci kaunar da yakemin ba, inasan ya rage san da yakemin ne saboda ko daga baya inyasan abinda ya faru bazai dameshi ba."
Jalila ta kalleshi kawai sai jitai tayi dariya, kallan mamaki ya mata yace "dariyar menene?"
Tace "yaya, wallahi rashin sakarma mutane fuska da zama cikin mutane yasa gaba daya tunaninka daban ne, kana tunanin wai abinda kakemai na zafi zafi shine sai sa ya rage sanka? Ko ya rage damuwa dakai?"-
Hassan ya kalleta cikin mamaki, tace "ashe ma gwara ni."
Fuska ya hade yace "gwara ke me?"
Tace shikenan.
Shiru yai baice komai ba ta kara cewa "tab lalai yau naji abinda ban taba ji ba."
Harararta ta yai yace "zaki cigaba ko?"
Ta rufe bakinta tace "bance komai ba."
Haka suka isa gida, suna isa suka shiga ciki, Abba na kallansu ta glass din falonsa, murmushi yai na jin dadi tare da godiya ga Allah.Suna shiga daki ta shiga toilet tai wanka saboda fashin sallah da takeyi, sannan ta fito ta dau bargo zata shimfida, kallanta yai yana zaune akan gadon yace "ki dawo nan ki kwanta yau ma a kasa zan kwana."
Tace " a'a ka kwanta."
Kallanta yai tace "in na kwana yau gobe ma anan zan kwana."
Yace "sanda na matsu da gadon sai na tureki na kwanta."
Tadan hade rai kadan tace "bari na dau hijabina na tafi gidan Goggo kafin ma a tureni inji ciwo."
Murmushi yai yace " wannan dai neman magana kike, matar dana kaiki har kofar gidan kikace bazaki iya rabuwa dani ba?"
Baki ta bude cikin mamaki tace "a yaushe akai hakan?"
Yace "musawa zakiyi kenan?"
Ta matso kan gadon wai ita a dole an ba ta mata rai ta kwanta tare da juya baya tace " wallahi na kula duk abinda banceba sai acemin nace."
Kallan bayanta yai ya tuno abinda ya faru a mota, kallanta yai yace "to ko mu sanar da Goggo laifin da mukai?"
Juyowa tai ta kalleshi tace "laifin me?"
Yace "na fitsarar da mukai......"
Da sauri ta mike tasa hannu ta toshemai baki tace "yayah."
Kallanta yai sannan ya zare mata hannun data rufemai baki yace "yanzu yanda kika hau kaina me kike nufi?"
Da sauri taja baya tace "wai ni yaya....."
Yace "wai a yaushe na zama yayanki ne?"
Baki ta turo tace "to ni me kakeso nacema?"
Yace "oho amma ni bansan yayan nan."
Tace " to naji ka daina tsokanata."
Fuska ya hade yace "a yaushe na tsokaneki? Bakiyi rashin kunyar bane? Ko yanzu baki hau kaina ba?"
Tace "kaine fa ka jawoni kamin kiss sannan yanzu bafa kanka na hau ba."
Kansa ya juyar gefe yace "ni? Kin tabbatar bake kika fara ba?"
Ta saki baki tace "yaya tanan ka bulo? Su biyu fa kenan kana min haka."
Murmushi ya sake yi.
Da sauri tace "yaya kayi murmushi wlh."
Shiru yai yana kallanta sai dai yanayin fuskarsa ya canza yace "Jalila!"
Gyara zama tai a hankali tace "naam."
Yace "nagode."
Kallansa tai cikin mamaki, yace "zan sanar ma Abba komai, ko tsanata zaiyi ko hukuntani zaiyi zan dau komai, nagode da kika budemin zuciyata