Showing 12001 words to 15000 words out of 44294 words

Chapter 5 - YAR ZINA CE COMPLETE HAUSA NOVELS BY MARYAM PINKY.txt

tsoro,ita kanta Asma'u sai da takusa sakin fitsarin don tsoro,farouq ma sai da ya toshe kunnuwansa don yadda muryar taringa amsawa,
Tashi yayi ya nufi gun da take ya dau wayar charger yana zuwa ya tsula mata yace "ist a toilet?" Ya fad'a yana qara zazzare mata ido,
Kuka take yi kamar wadda uwarta ta mutu,
Hannunsa yad'ora kan lips d'insa yace"shiiiiiiii"
Kamar an d'auke wuta tayi tsiit!..Ummah Rabee ce tashigo don jiyo kukan datayi,qarasowa tayi tana kallon su tace"meya sameta ne?"Abdul cikin kawar dakai ya juya ya koma kan kujerar sannan yace
"Fitsari tayimin a qasa,tafi da ita" murmushi ummah Rabee tayi tace "to" sannan takama hannun Kibdiyya tace "zo mu tafi kinji Matar Abdul" gocewa tayi alamar bazata ba,Aikuwa ya taso riqe da charger yanufota,da sauri tafice itama ummah Rabee tabita tana murmushi, dubansa yakai gun Asma'u yace"sai ance ki tafi ko?"da sauri ta tashi tafice,tsokiii yaja ya shige bedroom yabar farouq anan,
Shima bin bayansa yayi cikin bedroom d'in,A zaune ya hangoshi a bakin gadon ya dafe kansa da hannunsa,qarasawa farouq yayi yace
"U see..ka rage zafin rannan naka,kanka kake had'awa stress dayawa" cikin serious tune yayi maganar,zazzafan huci ya futar sannan yace "bani ruwa da tablets a drawer" miqewa farouq yayi ya d'auko mai ruwan a fridge sannan ya bud'e drawern don d'auko maganin...cak ya tsaya don ganin tulin qwayoyin kuma duk iri d'aya gasu birjik wasu ansha wasu ba'ashaba,guda 'Daya ya d'auko ya dawo kan gadon yabashi,yana amsa ya jefa 4 abakinsa ya 'Dora gorar ruwan sai da yakusa shanyewa sannan ajiye tare dayin gyatsa,shiru duk sukayi for some 25minutes sannan Abdul yadawo dai-dai,miqewa yayi ya je falo ya d'auko breakfast d'in yadawo qasa ya zauna,yafara zazzubawa,kallon farouq yayi daya zubo masa ido yace "Join me",sakkowa farouq yayi suka fara cin Abincin, Sai da suka gama suka kawar da kayan sannan suka zauna,
Abdul ne yace"On Monday zamu fara zuwa Bank"
Farouq yace "Allah yakaimu,First bank d'in"?
Girgiza kai yayi yace " Central"
Numfasawa farouq yayi yace "story nazo fad'a maka naga kana ta masifa" murmushi Abdul yayi yace"kai dai bari,wai ni Husna zata nunawa ta girma"
Yafada yana jijjiga kai,
Dariya sosae farouq yayi yace "see u,da bata girman ba?"
Shima dariyar yayi yace "Aikuwa nakoya mata lesson"
Duka farouq yakawo masa yace "Allah boss?"
Anan yabashi labarin abinda yafaru har wuyar da yasha,
Farouq banda dariya babu abinda yake,da kyar ya dai-daita yace "Haba no wonder naga Husna tayi wani so slowly, Ashe Maza takusa ji"yafad'a yana kashe ido,
Shidai Abdul baice komaiba,farouq yacigaba cikin serious mood yace" Amman Abdul yaushe kafara shan tablets?"
Siririn tsokiii yayi yace "mtsww since in Holland"
Cikin Jimami farouq yace "kadena shan su wallahi suna da bad side effect"
"I knw,ba yadda zanyi ne"
'Bata rai farouq yay yace"which kind u don knw what 2 do"
Gira Abdul ya d'aga mai yace "okay so kake naje nakama yaran mutane ina raping d'in su"?
No Yakama ta yanxu ayi bikinku da Husna friend,
Numfashi yaja sannan yace "uhmm Nima nayi tunanin hakan"
Murmushi farouq yayi jin yayi Nasara yace "thaz d best solution ma safe....Any way dama zuwa nayi nafad'a ma remain 3weks 2 my marriage" zazzaro ido Abdul yayi yace"A re u serious?" Ido farouq ya d'aga yace "sure"
Hannu ya miqo masa yace "congratulation" murmushi yayi yace "tnx u" da haka suka cigaba da firarsu irin ta Abokai ..
_*Pinky ce*_
[1/26, 3:01 PM] maryam Tahir Author Y4: *YA'R ZINA CEšŸ‘„*
_......Adulterer's Daughter_
*A True life, touching hrt & luv story*
_BY_
*MARYAM PINKY*
www.Maryampinky.Facebook.com.
1⃣4⃣
"who d u hate?,Asma'u?"ya tambayeta cike da tsananin mamaki, Dan shi yanxu mamaki take bashi sosae,Turo baki tayi gaba tace
"Eh..itan"
Kallon baki da hankali yake yi mata sannan ya girgiza kai yace
"Olright,me tayi miki kika tsanetan"?
Anzo wajen Dan gyara zama tayi ta kalleshi tace
"Ba ita ce wai zata aure kaba"
"Uhumm,sai akayi me?" Shima ya tambaya cikin tsinkewar zuciya,nok'e kafad'a tayi tace
"To ni banaso ne"
"Why"? Ya tambayeta
Shiru tayi Dan ba amsa,Numfashi yaja ya futar sannan ya miqe yace " tashi mutafi cikin"
Nok'e kafad'a tayi cikin muryar shagwab'a tace
"A'aa ni sai dai ka Goya ni a bayanka ka kaini"
Baki ya saki galala yana kallonta cikin zuciyarsa yake cewa "lallai yarinyar nan yazama dole ma su Abba suyi breaking auren nan,Dan naga nema take tafara kawomin raini,..wata xuciyar kuma tace ka kyaleta jinin _Anty Aisha_cefa"wayoyinsa ya d'auka daga bedside table batare daya kalli inda take ba yafice,direct falo ya wuce cox yasan su mummy suna can,da sallama yashiga falon,duk suna zaune suna kallo,daga gani breakfast suka gama,Duk suka amsa masa suna murmushi xuciyoyinsu cike da qaunar tilon 'Dan nasu,1seater ya nufa ya zauna yana cewa wash! Nagaji fa mummy,dariya Abba yayi yace "sannu son" itama mummy tayi masa,bayan ya gaishesu ne Mummy ta kalleshi tace "Son Husna kuwa ta sanar maka zasuzo"?
Batare daya dago ba yace
"uhmmn"
Murmushi Abba yayi yace
"Okay shiyasa yau kaci kwalliya haka daman?, kace zance za'azo maka"
Dariya mummy tayi tana kallon Abdul da yayi reacting kamar badashi ake ba,
Mummy tace"Aikuwa dai,kuma kasan akwai ma Uwargidan anan"
Duk suka saka dariya banda shi,don idan da sabo yasaba da tsokanar Abba da mummy,muryar Abba yajiyo yana cewa
"Ahh,na mantafa akwai madam Rigima"
Mummy zatayi magana kenan sai gata nan tashigo tana kuka,duk suka kalleta suna tambayarta "Lafiya"?,
Gun Abba taje ta zauna gefenshi setin kujerar da Abdul yake tace
"ba Yaa Abdul bane nace ya Goya ni ba ya taho" tafada tana nunashi da hannu,
Dariya mummy tayi tace
"Son meyasa baka Goya taba.." Sallamar su Asma'u da mummynta yasa duksukayi shiru,da sauri mummy ta tashi ta taro Aminiyarta tana yi mata barka da zuwa,zama sukayi kan 3seater suna murnar ganin juna,Asma'u ta qaraso falon kanta a qasa sanye take da doguwar Riga bak'a mai Stones pink,tayi rolling kanta da veil din,lips dinta sunsha 24hrs pink color,har qasa ta tsuguna cikin ladabi ta gaishe da Abba,yana murmushi yana Amsawa yana tambayar ta karatu,miqewa yayi bayan sun gaisa da Hajiya Bilki ya haura upstairs, Abdul kuwa da tun shigowarsu ya zubawa Husna ido Dan ba k'aramin kyau yaga tayiba,gashi tayi wata irin cika kamar ba YA'R 22yrs ba,kallon seconds yayi mata ya dauke kai Dan karta ganshi,amman cikin zuciyarshi soyake yasake kallon ta,Dan ba qaramin kasala ta saukar masaba gashi sai qamshi take,itanma agunta hakane don xuciyarta ce tadinga harbawa tinda ta shigo ta hangoshi,"he's olways cute"tafada a hankali,cikin xuciyarta kuwa wani son shine yake mata yawo,
Tsugunawa tayi tana gaishe da mummy "Ina wuni mummy" tace,
Da murmushi mummy ta shafa kanta tace "lfy low daughter,y studies?"
Cike da kunya take amsawa "Alhamdulillahi mummy"
Hajiya Bilki ce takai dubanta ga Abdul daya wani tsare gida tace
"Mutanan Holland andawo Lafiya"?
Shafa fuskarsa yayi ya 'Dan saki fuska ya gaisheta sannan ya miqe yafice,Aikuwa da gudu Kibdiyya ta Mara masa baya,
Sai A lokacin suka kula da ita,murmushi Hajiya Bilki tayi tace
" Hajiya Kibdiyya an zama ya'n mata"
Mummy ce ta kalli Asma'u da yanayin fuskarta ya 'Dan canza tace
"Uhumm wllh kuwa kinganta nan sai rigima,yanxu ma yi sukeyi kuka shigo"
Dariya Hajiya Bilki tayi tace
"Ina ruwan Kibdiyya, ni bata bari ma mun gaisaba,kodan taga yafita"
Kawai rigimace wallahi irin tata,wai sai Ya Goya ta Dan fitina irin tata ina SON ina goyo,
Murmushi Hajiya Bilki tayi tace
"Yarintar kenan ae"
Mummy ce tace"Daughter d'auko flasks d'incan ki kaiwa son,break yashigo yi bata bari yayiba",
Asma'u cikin murna ta miqe ta dauki tray din duka tatafi part dinsa,da kallo suka bita duka,cikin zuciyar Mummynta take tausayin d'iyar tata yadda take son Abdul har baya b'oyewa,itakuwa mummyn Abdul murna ce fol cikin xuciyarta ganin yadda Asma'u ke son 'Dan nata,
Mummyn Asma'u ce ta kalli mummy tace "Hajiya Nifa zuwana da biyu nazo"
Dariya mummyn Abdul tayi tace "I see,tashi mu haura sama"
Duk suka miqe suka nufi upstairs,
Suna shiga suka zazzauna sannan mummyn Abdul tace
"To Aminiya inajinki"
Lemo Hajiya Bilki ta kurb'a sannan ta ajiye tafara magana
"Am..wato Hajiya Daddyn Husna ne ya Aikoni,kuma dai akan maganar yarannan ne wato Abdul da Husna, wallahi Hajiya fada miki ne banayi amman kusan tin last year ya matsa sai yayima Husna Aure,convincing d'insa nadinga yi,tofa tinda yaji labarin dawowar Abdulkarim yaketa mita wae lalle yabamu 2month ayi aurennan,inba haka ba shi zaibata wanda yagadama...to kinji dalilin da yasa na garzayo Dan mu san abinyi" Ajiyar zuciya Hajiya Amina tayi sannan tace
"Kai amman fa naji dad'in labarin nan, kamar kinsan jiya Abbansa yake cemin Angama ginin gidan yaushe za'asa biki"
Cike da Annushuwa mummyn husna tace
"Allah Hajiya?,kice Anyi akan gab'a?"
Tafawa sukayi sannan mummyn Abdul tace "wllh kuwa,don haka tashima muje gun Alhaji yaji Dan na san sai yafini farinciki"
Hajiya Bilki tadubi Mummyn Abdul tace
"Amman fa wani hanzari ba gudu ba.."
"Name fa?" Inji Mummyn Abdul,
Numfashi taja cikin kamar rad'a tace
"Auren sa da Kibdiyya kuma yaza'ayi dashi ko kawae shikenan?"
Shiru tayi Dan tanajin nayin fadar Amsar,amman sai ta dake tace
"Ai inaga kawae su biyun zai bari,saboda Kibdiyyan naga tana sonshi,"
Ba haka taso ba,taso ace yarinyarta ta ita kadai zaiyi amman ba komai haka Allah ya tsara,
"To shikenan"
Miqewa sukayi suka nufi part din Abba.
Shi kuwa Abdoul yana fita part dinsa ya koma cikin falon ya yada zango,cike da kasala ya zauna akan lallausan rug d'in ya d'ora kanshi kan kujera, wani irin yanayi yake jinsa,cikin zuciyarsa yake tambayar kansa _"Dama haka Husna ta koma?,to yaushe?"_bashi da amsa sai kawae ya lumshe idonsa yana tura hannunsa cikin sumar kansa don jiyakeyi kamar kiyashi kebinsa,surarta ce kawai ke gilma masa,OMG! Ya fad'a yana dafe kansa don jiyo jiniyar kukan Kibdiyya ta nufo falon,zamewa yayi ya kwanta akan rug din ya rintse ido Dan jin yadda mararshi ta qulle,tana zuwa kwanciya tayi akan ruwan cikinsa ta kifa kanta tana cigaba da kukan,shafa bayanta yashigayi A hankali yace mata cikin kunne "sleep pls" shiru kuwa tayi tashiga sauke ajiyar zuciya,sanyi yafaraji yana busashi ga haqoransa daya fara rawa kaf-kaf,tashi yayi da kyar ya sata a kafadarshi yashiga bedroom suka kwanta,A.c ya rage sannan yadauko blanket yarufe kansa duka,
_*Pinky ce*_
[1/26, 3:01 PM] maryam Tahir Author Y4: *YA'R ZINA CEšŸ‘„*
_......Adulterer's Daughter_
*A TRUE LIFE, TOUCHING HRT & LUV STORY*
_BY_
*MARYAM PINKY*
*®REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*
_{We don just entertain nd educate,we touch the heart of readersā¤_}
#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*IG PML WRITERS*
#https//www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com
*1st JANUARY, 2018*
*Masoya,qawaye,ya'n uwa Allah yabar qauna,baki bazai iya fad'ar yadda kuke qaunataba,ina jin dad'i sosae,kuyi haquri bazan iya lissafakuba kunyi yawa,amman Nima ina sonku sosae...HAFSAT ZABOOR,MAMAN ZARAH,FARYNCY,da..da...kashļ¤¦ļ»ā™€ kunyi yawa da duk members na* _*PINKY NOVEL FANs 1&2,MARYAM SALISU MAI DALA,KHALEESAT HAYDAR,ZUWAIRAT UMMU MARYAM,MZZ DADY NOVEL,COOL NOVELS(yaya Hayat),ZEE MAKAWA NOVEL(Takari fan's),FEENAT JA'AFAR NOVEL,HAUSA NOVELS(Sadiya zaboora)...groups over & NURSE HALIMA(Niger), Anty Khadeeja(National hospital Abuja).....Dan Allah kuyi haquri kunyi yawa wallahi bazan iya lissafoku ba😭😭,Amman wallahi muna tarešŸ¤šŸ¤*_
```JINJINA & SADAUKARWA```
_*P.M.L. dukkanku,FATY AZLAND,SADNAF,MOMYN SULTAN,ETNEEY,ROUKI KZIEe(Allah yasa na fad'a dai-dai),Billy show,Bilkee shwerh,faridat,fannah......kuma kunyi yawa Amman ana tarešŸ¤ā¤ā¤*_
1⃣7⃣
Suna Isa _Sokoto Road_ Anguwar Su K.B sukayi Parking awaje kasancewar akwai Jefi-jefi Jama'a masu zuwa,bayan Ya kashe Motar ne Ya kalli Abdul daya cika yayi Fam! Ya watsar sannan yace
"Idan ka gadama kafito"
Ko kallon sa baiyiba saima juyar da kansa yayi gefe,girgiza kai Farouq yayi kawae ya bud'e ya fice,sai da yagama yangarsa sannan yafito yaga Farouq d'in a tsaye jikin motar da Alama shi yake Jira,muryar Farouq yaji cikin sanyi yace
"Muje"
Batare dayace komaiba suka fara tafiya Zuwa cikin gidan,direct sitting room suka yi,da sallama suka shiga cikin,bakowa sai Mahaifinsu K.B da wasu mutane uku a zazzaune,cikin girmamawa suka tsugunna suka gaishesu tare dayi musu ta'aziyya,shima da hannu bi-biyu da fara'a yadinga Amsa musu tare da tambayar su iyayensu,
Farouq ne yad'an shafa kai yace
"Alhaji...Kabeer d'in yananan kuwa?"
Alhaji yace
"Eh...amman ya d'an raka wasu abokansa yanxu xaidawo kud'an jira.."
Cikin girmamawa Farouq yace
"Ba damuwa Alhaji"
Daga nan sukayi shiru...sai su Alhaji da suke Hirarsu jefi-jefi,can 'Daya cikin Abokan nasa yace
"Alhaji a d'auko Yarinyar muyi Addu'a,
Hucin 'Bacin rai yayi sannan yazaro Wayarsa ya daddanna ya kara a kunnensa... Can yace
"Kibawa Aisha Jinjirar takowo ta sitting room"
Numfashi ya sauke yace
"Gatanan za'akawo ta"
Shiru falon yayi na wasu mintoci..can saiga yarinya daba zata wuce 16yrs tashigo hannunta riqe da babyn an nad'ota cikin farin showel,da sallama tashiga ta tsugunna agaban Alhaji tace
"Gata Abba"
Batare da ya kalla ba yanuna mata Abokansa da hannu yace
"gata basu ita.."
Yafad'a zuciyarsa cike da qunci..wai yau shi aka haifowa jika YA'R ZINA...wannan abin kunya har ina? Kuma wai a cikin gidansa za'a raineta..tunanin sa ne ya katse lokacin dayaji d'aya daga cikinsu Yanata yi mata Addu'a... _"Allah ya Rayata bisa sunnah,ya Albarkaceta,yasa mai temakon Al'umma ce.."_ haka yadinga yi mata Addu'a 'Dayan yana amsawa tare da Farouq sab'anin Alhaji da Abdul,Kabeer ne yayi sallama cikin sanyi sab'anin da,guri yasamu ya zauna shima aka qarasa Addu'ar dashi,Alhaji(Abbansa)ne ya miqe yafice wanda yasa duk suka bishi da ido,A hankali Kabeer ya sauke idonsa qasa daya cika taf da qolla...Abokan Abbansa ne sukayi masa ta'aziyya suka miqo masa jinjirar,kasa karb'a yayi,sai Farouq ne ya karb'eta yana sake lullub'eta da towel d'in tanata bacci abinta,
Kukane ya kufcewa K.B bayan fitarsu mai cin rai,bubbuga kansa yashigayi a jikin kujerar dake kusa dashi yana fad'in.... _Astagfirullah ya Allah, Allah yajiqanki Hafsa...baki da laifi ni na tursasaki..Gashi kin tafi kinbarni cikin wannan duniya da babu Abinda ke cikinta sai Rud'ani,..kintafi kinbani hafsa..me xan cewa yarinyar nan idan tagirma..._bai qarasa ba Abdoul yatashi tsaye cike da fushi ya isagun K.B daya fara fita daga hayyacinsa,yana zuwa baiyi wata-wata ba ya 'Dauke fuskar K.B da mari mai tafiya da Hankalin mutum,yakuma 'Dauke shi da wani Marin dayafi na da sannan yasa hannu 'Daya ya damqo wuyan rigar k.b ya miqar dashi tsaye ya matse shi da bango Yana fitar da numfashi d'ai-d'ai duk jijiyoyin jikinsa sun tashi ga wasu hawaye masu zafi da d'umi dake kwaranyowa daga cikin idonsa daya rine yakoma kalar jaa,cikin tsananin wahala K.B ke sauke numfashi Dan matsar bata wasa bace,A cikin Wannan yanayin yaji Abdul d'in cikin tsawa da rawar murya yace masa
"Meye Ribarka!?,Meye Ribarka!!?,..K.B Yama kasa magana don Abdul d'in ya riqe masa maqoshi jiyake kamar zai mutu don Azaba,GARAM! Kakeji ya buga kan K.B da bango yana sake maimaita masa tambayar,tuni K.B yafara ganin duhu don Azaba,
Cikin sarqewar numfashi Abdul d'in yaci gaba
" Yanxu meya Amfaneka!,ka lalatawa yarinya rayuwa har shegen sperm d'in ka yashiga tasami juna biyu After all wajen haifar maka shegiyar Ya'r taka ta mutu!,me zata cewa Allah?, Kayi dai-dai kenan?!!!,K.B rayuwarka bata da Amfani..I hate u k.b,baka da Amfani tinda gurb'ata Al'umma kuke da Samar da Ya'ya bata hanyar Allah b,ba ka da Amfani K.B..sai na kasheka.....!!!,"duk yafita hayaccinsa banda kai kawo babu abinda Maqoshinsa keyi,ga pulse d'insa daketa bada loof nd doop sound at the same tym... Ganin Abin bana hankali bane yasa Farouq dayake riqe da yarinyar miqewa ya ajiye ta yaje gun ya b'anb'are K.B daga hannunn Abdul d'in da kyar,K.B daya fara jiyo qamshin mutuwa yafad'i gefe yana nishi yace "fa..fa..Farouq.. Ka..bar..shi ya..kasheni...rayuwa..ta..bata ...da Amfani...naqi jin shawarar Ku...yanxu..gashi..ina cikin dana sani..ka..barshi.." Sai kuma ya kife a gun ya suma,cikin tsananin rud'ani Yayi kansa amman inaaa ya suma,ruwa ya d'auko mai sanyi ya dinga kwara masa amman har roba biyu bai taso ba,cikin tashin hankali ya nufi hanyar fita don kirawo tai mako sai yajiyo shi yana Atishawa mai qarfi,da sauri yakoma gunsa ya d'agosa yana shafa kansa yana yimasa sannu,saida sukayi kusan 40mins ahaka sannan K.B yadawo hayyacinsa..,A hankali ya ruqo hannunsa ya matse cikin nasa yana hawaye ya furta
"Farouq ina yake?"
Sai lokacin Farouq ya kula Abdul bayanan,shiru yayi yana kallon sa, runtse ido yayi cikin Azaba yasake cewa
"Ya tafi ko,"
Kasa bashi Amsa yayi sai kallon sa dayake tayi cike da tausayin Kabeer d'in..
Jiyayi yakife kan cinyar Farouq yasaki kuka mai ban tausayi, cikin kuka yafara magana..
_"wllh Farouq bantab'a yin dana sani a rayuwa taba irin wannan, sai yanxu nagane abinda kuketa gayamin,kaga ranar da Abdul yake fad'a min tazo ko?,Na tabbatar bani da masoya sai ku ,Abdul yafice Aboki sai d'an uwa,Dan Allah ya zanyi Abdul ya yarda dani?yazanyi ya yarda na tuba?,.."_kuka yaci qarfinsa yakasa qarasawa,bubbuga bayansa Farouq yadinga bubbuga bayansa yana kwantar mashi da hankali yana cewa
"Kayi haquri..kayita istigfari Allah zai yafe maka,baka makara ba,shi maji roqo ne kuma mai yafiya ne,kai dai ka tsarkake niyyarka,"
Hawaye ya goge sannan yasake
"Abdul fa..?"
Shiru yayi na d'an secnds sannan yace
"Abdul zai huce amman ba yanxuba kasan shi da xafin rae,amman nasan zai huce"
d'aga kai yayi yana jimanta Al'amarin,
Farouq haka yayita convincing d'insa har yasamu peace of mind sannan suka miqa YA'R ciki suka fito suka koma gidan su.
****************************
Abdul cikin tsananin b'acin rai yafice daga gidan su K.B ko gabansa baya gani sosae,banda tafasa ba abinda zuciyarsa keyi ga wani irin sarawa da kansa keyi kamar zai rabe biyu,da kyar ya Isa gida,security ya bud'e masa gidan yana yi masa sannu da xuwa ko ta kanshi baibiba yashige ciki, A harabar yaga motoci anyi parking da alama Abba ne yayi baqi,da niyyarsa yaje gun mummyn sa koyaji relief amman yasan tana tare da kosuwaye yanxu don haka ya juya ya nufi part d'insa, yana shiga ya Mirza key don baya buqatar komawa,ko takalminsa bai iya cirewa ba yafad'a kan makeken gadon sa ya kwanta rubda CIKI ya lumshe ido,babu abinda yakeyi masa yawo a zuciya irin gaba d'aya Al'amarin Kabeer Abokinsa,gaba d'aya tsanarsa yakeji,shi a rayuwarsa yana matuqar kishin Addinsa,shikuma mai kyankyamine,baya san qazanta kuma musamman ta ZINA, runtse ido yayi jin kansa yada d'a sarawa ta gefe,Gani yakeyi kamar yanxu Kabeer ya lalata Hafsa,da haka bacci mai nauyi ya d'ebeshi.
**************************
Husna kuwa tana fita daga d'aki lokacin da Abdul ya koreta upstairs ta koma tasami su mummy suna firarsu,canza mood dinta don karsu gane abinda yayi mata don ko kad'an batason mummy tasan abinda Abdoul yake mata,tabarwa xuciyarta don su Rukky suna qarfafarta cewa idan sunyi Aure duk zai daina don sai yadda tayi dashi,da irin Wannan kalaman take samun sanyi a xuciyarta kuma take jin yardar zancennasu kuma tashirya d'aukan ko mai nene indai zai aure tan,kallon ta duk sukayi ita kuma sai ta qirqiri murmushi a fuskarta tace
"Am..em..mummy dama su Fadeela da Rukky ne sukace min sun taho zamuyi Assignment d'inmu..so I'm living.." Tafad'a tana rataye Jakarta..
Murmushi mummyn Abdul tayi tace
"Daughter baza kice musu gun mijinki kikeba suzo kuyi anan?." Tafad'a cikin wasa
Sunkuyar da kai Husna tayi tana murmushin da baikai zuciba, cikin zuciyar ta tace"hummn baki son meya min bane da kince na tafi"
Mummyn ta tace
"To Allah yatsare ki kula"
Ficewa tayi tana cewa "to mummy"
Mummyn Abdul tafito hannunta riqe da Leda madaidai ciya tana cewa "to daughter ga.." Turus tayi ganin sai mummyn ta,
Dariya mummyn Husna tayi tace
"Ae idan K'awayen nan nata suka kirata bata ji bata gani"
Dariya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login