Showing 57001 words to 60000 words out of 100116 words

Chapter 20 - UMMIE Hausa Novels PDF By Autar mama.txt

10 Nov 2025

3443

kwantar da kanta ta ce " Shikenan ranka ya dade fushi ya kare"

Zayd be ce komai ba ya ajiye wayarsa ya cire rigar jikinsa. Zagayowa tayi gabansa tana tsugunnawa ta ce " Na baka hak'uri fa"

"Na hakura ai" Ya fada ba tare da ya kalleta ba.

"OK ni menene laifina? Bansanfa zai zo ba kawai zuwa yayi"

Zarah ta fad'a tana kallonsa. "Shikenan ai bana fushi dake bana dai so ya kara zuwa zan kirashi anjima"

"Tohm muje kayi wanka"

"OK" Ya fad'a yana kallonsa.

Sun d'au lokaci a dakin kafin su fito Ummie har tayi bacci a kasan rug ga abinci a kusa da ita.

Murmushi Zarah tayi tana d'aukarta ta mayar kan kujera. "Su Ummie gashi ya fito" Zayd ya fada yana dariya. Zame dan kwalin kanta Zarah tayi aikuwa ga gashin nan ya fito sosai duk da be kai na da tsaho ba. Ai kuwa idan ta karayiwa yarinyata aski zata gani"

Zarah ta fada tana dariya.

"Dazu munyi waya da Zainab wai zata kawo miki Aisha ta tayaki zama ki dandana kiji"

Cewar Zayd yana murmushi. Dining Zarah ta nufa tana fad'in " Munyi maganar ta whatsapp nima haka nasha wannan wahakar da Ummie lokacin tana karama bama bacci saboda kuka kuma ba ciwo ba ba komai ba tsabagen rigima"

"Kema haka kikayi ai" "Kaima nasan haka kayi" Ta fada tana murmushi. "No ki tambayi Aunty ni yaro ne me hakuri kanar dai yadda nake yanzu"

"San kai ko? Girgiza kai yayi sannan ya ce " Ko daya gaskiya ce kawai"

"Shikenan damo.... Zarah ta fada tana isowa inda yake.

Ita ta ciyar dashi suna hira gwannin birgewa.

Rayuwarsu a yan kwanakin da Ummie ta zo ya sauya sosai sunji dadin zuwa Ummie dan tana basu nishadi da surutanta ko sau daya bata taba fadar abinda Aunty Sa'adah take ma ta ba na tsawa da hantara da yawan taba ma ta jiki da Saleh yake yi ita kuma Zarah bata tambayeta ba tana ganin kamar idan tayi hakan bata kyauta ba duba da yadda Ummie tayi kiba bata da alamar damuwa a tattare da ita.

Ranar lahadi da yamma Zarah tana jiran Sa'adh tazo ta d'auki Ummie dan Shehu ya kirata yace ita zata zo.

Shuru² bata zo ba har kusan magariba. Horn din motor da ta ji ya sa ta gane cewa Sa'adah ce dan wannan ba horn din motar mijinta bane.

Tana zaune tana gyarawa Ummie kitson bid din da kaita saloon akayi dazu da rana duk da bata so taji muryar Shehu a tsakar kanta.

Da sauri ta kalleshi tana tashi tsaye ta ce " Kai kuma haka ake yi ka shigowa macen auren d'aki?

Kallon Ummie yayi yana fad'in zo" Ba musu ta isa inda yake hankici ya ciro a aljihu ya ce "goge hancinki"

"Abba babu majina fa" Ummie ta fada tana kallonsa. Ganin ya had'e rai ya saka ta karba ta fara goge hancinta. In few seconds Ummie ta nemi faduwa kasa da sauri Zarah ta isa inda take tana riketa kafin wani lokaci Ummie ta rufe idanunta.

"Me haka?! Ta fada da karfi Jijjiga Ummie.

"Don't you worry in few hours zata tashi"

Kain Zarah ta ankara taji ta tsohe ma ta baki da hankici.

Fun daga lokacin bata sake sanin inda kanta yake ba.


Tana bud'e idanunta taganta a gidan Aunty. Kanta taji yayi wani irin sarawa, da sauri ta rufe idanunta tana dafe kanta.

Aunty ce ta fito daga daki tana kallonta. "Zarah! Ta kira sunanta.

Zayd ya yake daki yaji Aunty ta ambaci Zarah, zuciyarsa ce tayi wani mugun bugawa tana masa wani radadi da zafi.

"Zayd! zo zarah ta tashi"
Cewar Aunty daga chan falo.

Lumshe idanunsa yayi yana tuna yanayin daya ga matarsa da tsohon mijinta, "How dare she! Ya fada yana ture kwanukan abincin da yake gabansa.

Sake kiransa Aunty tayi da kyar ya amsa yana fitowa.

Idanunsa sunyi ja sosai. Sam Aunty bata lura da yanayinsa ba sai murmushi take tana kallon Zarah.

Da kyar Zarah ta iya zama tana jin jikinta wani iri ba dad'i.

"Ta shi mu tafi gida"

Ya fada yana kallonta"

"Haba Zayd wani irin ta tashi ku tafi kana gani kamar zata fad'i daga zaune"

Aunty ta fada tana kallonsa.

"Baice ko mai ba ya fara latsa wayarsa kafin ya kara a kunne ya ce " Ina jiranka yanzu"

Sauke wayar yayi ya kalli Zarah ya ce " Kisa hijabi driver zaizo mu tafi"

Tashi Aunty tayi ta nufi kitchen ta kawo ma ta ruwa da kunu, da kyar Zarah ta iya sha ganin yadda ranta mijinta yake a matukar b'ace.

Sam ta kasa tuna me ya fara da ita.

Driver yana zuwa Aunty ta taimaka ma ta zuwa mota.

Har suka isa gida babu wanda yace da wani k'ala.

Da kyar ta iya kai kanta falo.

Zama tayi a kujera tana jin kanta na ciwo sosai, a hankali ta kwanta bata dade ba bacci ya dauketa.

A gaba ya sata yana kallo! "Fushin me yake yi? Zarah zata iya aikata abinda yake tunani?

"Zata iya mana! Zaman da kuke yi da ita ai baka iya sauke wani hakkin na ta ka kasance mara lafiya ita kuma mace me lafiya" Yaji wani bangaren na zuciyarsa ya raya masa.

Runtsa idanunsa yayi da sauri, Shehu kawai yake hangowa rungume da matarsa a kan gadonsu na Sunnah daga ita sai vest da wando da kadan ya wuce gwiwa.

Kalamar innalillahi wa inna ilaihi raji'un kawai Zayd yake maimaitawa.

"You idan Act Shwhu yake yi meyasa daya ganshi zai firgita?

"Sun aikata zina ne? Da sauri ya girgiza kansa yana runtsa idanunsa baya son yana wanna tunanin akan matarsa amma abun zai iya yuwa duba da cewa wajen 8months babu abinda ya shiga tsakaninsa da ita tun na farko kuma a iya zaman da sukayi da Zarah ya lura da yanayinta sosai"

"Zarah why! You should've told me! Da kin fada min Zarah! Wallahi dana sakeki! Ya fada yana jin zuciyarsa nayi masa wani radadi.

Kwallar data zubo masa ya goge da sauri yana kallon fuskarta, "Tana dawo wa hankalinta zai saketa lefinsa ne tun farko da bai saketa ba har ta kaiga faruwar hakan, bazai iya fadawa kowa wannan lamarin ba har Aunty dan yana ganin kamar ya tonawa matarsa ne asiri so zai ajiye maganar iyaka zuciyarsa.

Wayarsa ce ta fara kara dubawa yayi yaga private number ce, sai data kusa katsewa sannan ya d'auka.

"Oops, Auchhhh da zafi ko? An fad'a maka haka ake renon mace? Ka kyale ma ce da tarin ni'ima desire! Amma kana cutar baiwar Allah! Oh ashe fa ba lafiya yin abun! shikenan ai bakomai na dai sauke ma ta duk wani sha'awa da take dakonsa a daren jiya, i really missed her tes... Be jira ya karasa ba ya kaste wayar yana wurgi da ita zuciyarsa na tafasa, be taba jin bakin cikin rashin kafafaunsa ba irin yau! Da ace yana da kafafu da shehu ya gane kuransa. Sosai maganunsa suke dawo masa a zuciya, meyasa Zarah batayi kokarin kwatar kanta ba! Tahat means tana so? Girgiza kai yayi da sauri yana son kin yarda da abinda zuciyarsa take raya masa amma wani bangaren shedan na kara cusa masa tabbacin abun.

"Meyasa Zarah zatayi masa haka! Ya dawo da ita gida dan ya tambayeta amma yanzu shehu ya tabbatar masa da zarginsa.

(Yanke hukunci ba tare da dogon nazari da bincike ba yana haifar da dana sani kuma abinda Zayd zeyi kenan)

*Please just be patient, kuma ina so ku gane bawai zan gina labarin bane a soyayya gaba daya, and remember one thing sun an book din my Ummie ba Zarah ko Zayd ko shehu ba! Nasan Zarah deserves happiness but Karku manta jigon mu Labari akan soyayya da kuma kalubalen rayuwar, wallahi wani zaizo duniya tun yana karami yana shan wahala har ya koma ga mahallicinsa so inaso ku gane duk da cewa wanna novel ne but zan tafiyar dashi kamar gaske i mean abubuwan da suke faruwa a rayuwar mu ta yau da kullum iya daidai fahimta, ina fatan zaku fahimta nagode*

Autar Mama ce
✨✨ *UMMIE* ✨✨

_Labari daya danganci soyayya da kuma ƙalubalan rayuwa_

*FREE BOOK*

*MALLAKAR*
*Autar Mama*

*EXQUISITE WRITER'S FORUM*
(E.W.F)

*Follow me on Wattpad @Autarmama56*

I just published "Chapter 23" of my story "UMMIE". https://www.wattpad.com/1189062978?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=AutarMama56&wp_originator=rD60tesU6CXFzWFomRxhLwAn9Cecr5TIWl3xjeqOX5rxv%2BKxlbZuUWup6RD5m%2Fk%2F7e1awX7GiBMS9TrjJqj6OfxLhZWM6ejm0cf6tOZ6NSXz0OHs2kHGY6mxQB9kD4Es

*Please subscribe, and like my YouTube channel*

https://youtu.be/9m2j2vaiKjw

Aslm ma abota biyan littafin Momin Haneef ce tana sanar daku littafin ta na ak'idar masarautar.

littafin nakud'ine idan kina buk'ata zaki iya fara biya tunkafin free page yak'are gamai son littafin ak'idar masarautar zai turo da kud'insa ta wannan account👇

Nusaiba Rabi'u Union Bank 0087778987

Idan kuma katine zaku turo katin MTN ta wannan number👇
07026368879

Bamuson vtu bazamu kar b'aba

Idan kinturo kud'in zaki turo mana da shaidan kin biya ta wannan number07026368879

Normal group 300 only
Zakuna samun page d'aya (1 )arana

Special group 400👇
Zakuna samun page biyu (2) arana duk Wanda kikaga yamiki sai kishi ga.

*Taurari biyu kuma Matasan marubuta masu tasowa Sunzo muku da dadadan wanda zai nishad'antar daku masoya wannan Matasan marubuta ba kowa bane illa: 𝙈𝘼𝙈𝘼𝙉 𝙉𝙐𝙎𝘼𝙄𝘽𝘼,,𝙄𝙆𝙄𝙇𝙄𝙈𝘼 𝘼𝘿𝘼𝙈(𝙠𝙮𝙖𝙪𝙩𝙖 𝙙𝙖𝙜𝙖 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 ) Sunzo muku da sabon novels masu suna.

*𝙈𝘼𝙈𝘼𝙉 𝙉𝙐𝙎𝘼𝙄𝘽𝘼* tazo muku da littafin (𝙆'𝘼𝘿𝘿𝘼𝙍𝘼 𝘾𝙀)

𝙄𝙆𝙄𝙇𝙄𝙈𝘼 𝘼𝘿𝘼𝙈( 𝙆𝙮𝙖𝙪𝙩𝙖 𝙙𝙖𝙜𝙖 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝) tazo muku da littafin (𝙆'𝘼𝙉𝙒𝘼𝙏𝘼)
Kai dajin sunan labarin ma kasan basai an tambaya ba.

*(K'ADDARA CE)*
*Dandano! Dandano!!*

Hanan meye lefin mu dan muna cikin garin Saudiya? Muma bayin kammu bane K'ADDARA CE ta kawo mu cikin Saudiya. Hanan mai muka yiwa mutane suke jifan mu da mummunan kalma?. Cikin masifa Iman Ta zaburo bata yi magana ba ta damk'i hannun Sultana Tace" Ke Sultana muje ki nuna a hanyar shara-mansoor d'in Uban waye ya fad'i miki wannan maganar yau saina wuk'ance shi fuuu suka bar Hanan anan tasaki baki...


*K'ANWATA*

*Dandano!Dandano!!*


Mama kina ganin Abun da Salma taimin? Kin kasa mata magama. Jijjiga Mama take yi tana kuka mai tsuma rai..Mama ta d'ago jajayen idanun ta da suka ciko da kwalla Tace Rahama kiyi Hak'uri kanwar kice... Sharr! sharr!! Idanun ta suke zubar da kwalla da radadi had'e da zallar bakin ciki,take kallon sama ta daga hannayen ta sama tare da fad'in. Ya Allah ya Allah ka gana ganin Abun da K'ANWATA taimun ya Allah ka..


Ga maru buk'atar wannan novels d'in zasu iya tuntub'ar wannan numbobin. 09069080725 our +966599791573


Nomal. guda d'aya N 300 ne

guda biyu N 500 ne


Special guda d'aya N 500 ne

guda biyu N 1000 ne


Zaki iya biyan kud'in ki ta wannan hanyar. 3115484026 Ikilima Adam first bank

✌🏼Fitattu biyu masu ban mamaki🫀Hakika babban goro sai magogin ƙarfe 😍, Hakk'un wani kaya sai amale ke d'auka🐫, Fitattu biyu👯🏽‍♀sun shiirya tsaf domin nishad'antar daku 🤓 sun shirya tsaf domin fadakar daku🧠 sun shirya tsaf domin dilmiya zuciyoyin ku cikin bege da shauk'in so💋💞, wohoho tabbas ️sahun giwa👣 mai ɓadda na raƙumi 🐪,Fitattu biyu😍✌🏼 masu tafiyar k'asaita, sheƙi, da walwali hak'ik'a koda kud'in ka saida rabon ka😘🏃🏽‍♀️ Fitattun Ƙarshen shekara😍 salon su daban ne dana sauran domin natsuwa da tunani sunyi aiki pure love and romance abun dai sai wanda yakaranta😍 maza ku hanzarta neman naku karku bari abaku labari🏃🏽‍♀️

#Oum Sumayya:- *GAMIN GAMBIZA*✍🏽 Nrml 300 Vip 500
#Oum Ikram:- *SOYAYYA CE SILAH* ✍🏽 Nrml 300 Vip 500

Duka biyu 400👌🏼
Vip 700👌🏼
Via 4210014214
Eco bank and send the evidence of payment via 08139624956
Or mtn/airtel credit via 07017296839 banda vtu hoton kati kawai!


*Shafi na ashirin da uku*

Wani kallo Sa'adah ta ke bin Shehu dashi ranta a matuk'ar b'ace ta ce "Na gaji da halinka wallahi da chan kasan kana sonta ka saketa? Ya za'ayi ace kana da mata kana tunanin matar wani? Wannan ai tsantsar jahilci ne"

"Ke?! Ni kike kira da jahili? Waye ubanki? Cewar Shehu yana kallonta idanunsa sunyi ja ransa duk a b'ace.

Matsawa tayi daga kusa dashi tana kara rik'e 'yarta sosai kafin ta ce " Allah ya baka hakuri"

Wani dogon tsaki yaja yana fitowa daga d'akin, kusan karo sukayi da Ummie dake rik'e da plate d'in abinci.

"Ke dan uwarki bakya gani? Matsawa baya tayi da sauri ta ce "Abba kayi hakuri" Tsaki yaja ya wuceta, ajiyar zuciya ta sauke me karfi kafin ta shiga d'akin tana fad'in " Aunty Sa'adah ga abincin"

Banza Sa'adah tayi ma ta, itama bata k'ara cewa komai ba ta fito, Saleh ne ya rik'ota yana fad'in "Ubanwa kika zaga d'azu?

Kwace hannunta tayi tana zuba masa harara da dara²n idanunta ta ce " Ubanka!

"Kut! Ni kike zagi? Ya fad'a cike da mamakinta. "Eh an zaga! Aunty Zainab ta ce idan kayi min rashin mutunci na rama" Daga haka ta wuceshi ta nufi kitchen danyi wanke².

Biyota yayi yana rude kofar kitchen d'in ya ce "Wa kika zaga?

Tsaki ta ja tana rike kugunta ta ce " Dan Allah karka dameni, me shan taba kawai"

Takalmin kafarsa ya cire ya kamota yana hade hannayenta ya matse karamin duwawunta ya daketa har sau biyu, duk da taji zafi kuma taso yin kuka amma ta daure, yana sakinta ta ce " Allah ya isa"

Matse ma ta baki yayi cike da mugunta ya ce " Mayya" Ya k'arashe maganar yana tureta.

Fad'uwa kasa tayi, hawayen da ta rik'e suka zubo ma ta, tsaki yayi ya fice kuka ta fashe dashi tana fadin Allah ya isanta da kyar ta iya wanke².



*INDIA*
*MUMBAI*
*ADITYAH HOSPITAL*

A hotel suka sauka, Farooq kuwa asibiti aka wuce dashi dan basu ma zo hotel din dashi ba.

Washe-garin ranar da suka zo k'asar sannan Zayd yaje asbiti, ita kuma Zarah da Ummie suna hotel.

Beji mamakin maganganun likita ba kuma hakan beyi wani affecting dinsa ba Yusuf ma yafishi shiga damuwa, magunguna ya rubuta musu sannan suka fito.

Da kan shi yake operating new wheelchair dinsa me tsada sosai dan tafiya yake kamar babur.

Bayan sun siyi maganin Zayd ya kalli Yusuf ya ce " Nagode Sir amma bana tunanin zamanmu a India zai canza wani abun, ko zuwa jibi ne nida Zarah zamu koma Nigeria"

"Shikenan Zayd, Allah ya baka lafiya" Da Amin Zayd ya amsa dan shi yanzu bai san ne zaicewa Zarah ba.

Yusuf ne ya sashi a mota sannan ya saka wheelchair machine dinsa shima ya shima ya fadawa taxi din inda zai kaisu.

Yusuf be dade ba ya koma asibit wajen Farooq, Ummie kuwa ganin Zayd ya dawo ya saka tayi wa Zarah sallama ta fito wajen hotel din dan bata jin zata iya zama a daki ita kadai.

Kusa dashi Zarah ta dawo tana rik'o hannunsa ta ce " Me likitan ya ce?

Murmushi yayi ma ta kadan yana shafa hannunta ya ce " Insha Allah zan samu sauki amma sai a hankali zuwa next tomorrow zamu koma gida"

"Shikenan Allah ya kaimu" Ta fada tana zame hannunta daga cikin nashi.

"Zarah" Ya kira cikin murya me sanyi.

Kallonsa tayi ba tare da ta amsa ba. "Meyasa bakya dariya?

Shuru tayi tana kallonsa, 'Ita ba yarinya bace tasan likita yace bazai k'ara tafiya ba shiyasa zasu koma gida amma ya b'oye ma ta"

Tafin hannunsa taji a kan fuskarta, da sauri ta kalleshi, fuskarsa d'auke da murmishi ya ce " Zarah kinsan hawayenki suna sa naji zafi a zuciyata ko? Shuru tayi bata ce komai ba.

Sosai tasaka yaji ba dad'i dan kuka ta fashe dashi sosai. Sai da tayi me isarta sannan ta rarrashi kanta duk yana kallonta.

"Zarah inaso ki sani ita rayuwa cike ta ke da jarrabawa kuma wannan jarrawaba ta ce ina fatan bazaki sagar min da gwiwa wajen cinyeta ba ko?

Tsgunnawa tayi a gabansa tana kallon cikin idanuwansa ta ce " Zayd dan Allah kar kace zaka rabu dani saboda wannan dalilin"

"Zarah! Kin taba ganin auren da yayi surviving a haka? Bazan iya sauke wasu nauyi nakindake kaina ba ko a addini kina da damar da zaki rabu dani, i can't move my legs Zarah! Ji nake kamar ba'a jikina suke ba! Bazan iya cutarki ba saboda san zuciyata"

Girgiza kai tayi tana fadin " Babbar cutar da zakayi min itace ka sakeni!

"Zarah zamanmu is impossible! Kina ganin zaki iya but baki san yawan shekarun da zan dauka araye ba sai dai ko inada gajeriyar rayuwa"

"With love impossible can become possible Zayd, please mu bar wanna maganar"

"Awwwwwn, so kina sona dama? Ya fada cikin son ya zolayeta.
"Stop joking" Ta fada tana tashi tsaye.

Rik'o hannunta yayi ya ce " Zarah" "Uhm" Ta fada tana kallonsa.

" Ina kaunarki" Murmushi tayi tana fadin " Ka huta bari na baka magungunan"

"Bana bukatar magani indai kina tare dani"
Ya sake fada yana murza ma ta hannu. Kwace hannunta tayi tana nufa toilet da sauri.

Kula tasha a toilet Lamar hawayenta zasu kare, yana jiyo sheshekarta sosai abun yake damunsa yanzu shi bazai ce ga damuwarta ba ta ce zata zauna dashi a haka but why? Kukan me take yi? What is the point of those tears of hers? Kodai bata son zama dashi amma bazata iya fada masa ba? Koma menene idan ya koma gida zaiyi magana da Aunty.

Sai da tayi wanka sannan ta fito sanye da towel tana d'an goge ruwan dake fuskarta. Idanu ya zuba ma ta kusan na minti daya kafin ya ce " Shine zakiyi wanka baki gayyaceni ba?

"Ai kayi kafin ku fita da Yusuf" "Wannan ai ban fita ba wanda zanyi dake nake so"

Sai a lokacin ta kalleshi tasan neman magana kawai yakeyi.

Girgiza kai tayi tana danyin murmushi, sosai yaji dadi sakin ranta da tayi.

Sai da tayi sallar azahar sannan ta kaishi bandaki ta taimaka masa ya kama ruwa sannan yayo alwala duka fito.



*NIGERIA*

8PM

Ummie ce kawai a falo tana aikin makaranta, Ilham dake rarrafe ce ta fito daga d'akin Sa'adah tana isowa inda Ummie take, Kallonta Ummie tayi ta ce " Wallahi idan kika yagan littafi sai na dakeki"

"Toh ko daketa kin daki wa? Kedai Ummie kin fiya mugunta" Cewar Saleh yana zama a kujera ya dauki Ilham dake botsarewa ya sauketa.

Sauketa yayi yana fad'in

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login