Showing 66001 words to 69000 words out of 322641 words
Chapter 23 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt
Zokaga kuka a wajen wadannan ahali musanmman na master, uwar tayi kuka kamar zata shide, fadi take allah ya isa tsakaninta da murtala, bazata ta6a yafemashi ba kuma tayi danasanin haihuwarshi datayi
Abu dai ba dadi, sai bayan an kukkulesu ne sannan aka samu wani yazo yafadama yan sandan gidan da su mastern suke kwana amma koda sukaje babu su babu alamunsu donma ga yadda suka iske dakin a hargitse wardrobe dinsu babu komai ya tabbatar musu sun gudu.
Hakan yasa aka baza matakan tsaro akoina harda tashoshin motoci da airport don kama wadannan shaidanun
*KAKA*
Kamar yadda mutanen unguwa sukayi alqawari saigashi suna gama sallar asuba suka sake taruwa don fita nemanshi
Kasa kansu sukayi kashi2 inda kowa da inda ya nufa yadda abin zaifi zuwa da sauqi sannan suka bazama
Kaka kau kallo daya zakamata tabaka tausayi saboda har ramar dare daya saida tayi
Kan kace me? Gida yafara cika da mata yan jaje, a unguwa duk inda ka wuce sai kaji ana labarin 6acewar Deen din Kaka mai koko.
Wajajen qarfe tara saura yansanda suka dira kofar gidansu Deen.
Nan suka nemi iso cikin gidan sannan suka shiga
Haka aka rakasu dakin Kaka inda take zaune ba uhm ba uhm uhm sai yar charbinta datake ja
Ganin yansandan hankalinta yaqara tashi jin maganar Deen ce takawosu
Saida suka kwantar mata da hankali sosai sannan suka sanar daita Deen na asibiti dukda basu fadamata halin dayake ciki ba
Nan take gida ya kaure da koke koke, Kaka nayi mutane nayi, yan kadan ne masu rarrashi
Haka Kaka tafito tana shar6ar kuka da ita da matar mallam Nasiru da Baaba Abu aminiyarta suka bi yansandan bayan kowacce mace tafito an rufe gidan
A motar ne matar mallam Nasiru ta bugawa mallam Nasirun waya akan anga Deen yana asibiti takuma fadamashi sunan asibitin
Su zee na zaune a waiting room tareda daddy su Kaka suka iso
Sosai Kaka ke kuka akan abari ta ganshi
Haquri akaita bata akan tayi Haquri likitoci ke ciki tabari sugama aikinsu
Dukda Hakan batayi Shiru ba sai kuka take tana su taimaka mata shi kadai gareta
Haquri duk akaita bata akan ta kwantar da hankalinta insha allah komai zaizo da sauki
Dakyar aka samu ta zaune tayi shiru Saidai kwata2 hawayenta sunqi tsayawa
Zuwansu Kaka ba qaramin sake dagulama zee lissafi yayi ba don itama kukan nata da akasamu yayi sauqi ta cigaba dayi, tanajin cewa duk itace silar komai, idan wani abu yafaru da Deen tasan bazata ta6a yafewa kanta ba
Ana haka su mallam Nasiru da kingin yan tawagar neman Deen din suka qaraso, nan aka hadu aka tsaya jiran tsanmmani... ✍️
Manage 👏 babu dai editing, mugun wuya yake mun aradu☹️
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:34 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
*025*
Sun jima anan sosai sannan likitocin suka fito daga dakin da aka kwantar da Deen din
Mutanen na kyalla ido suka ga fitowarsu duk sai suka tashi kowa cikin jiran jin abinda likitocin zasu ce
Matsowa kaka tayi gabansu likitocin cikin hawaye tace
"Likita ya ake ciki? Ina jikana? Meya sameshi?"
Shima daddy ya taso ya matso wajensu, zee a gefenshi itama cikin zaquwar tasan halin da Deen din ke ciki
"Dr how is he now?" inji daddyn
Family Dr dinsu dake kan gaba a kula da Deen din yace
"Alhamdulillah, ku kwantar da hankalinku. Insha allah zaiji sauqi kai yama ji sauqi insha allah, yanzu dai Alhaji muje office akwai bayyanan da zan maku gamedashi acan"
Caraff kaka tace
"harda ni za'aiwa bayanin, ni kakarsa ce bayada kowa saini nima banida kowa saishi ku taimaka ku fadamin wani hali yake ciki, ku kaini wajenshi don Allah" ta qarashe tana rufe fuska da gefen zani
Dafa kafadarta Baaba Abu tayi cikin sigar rarrashi itama tana matsar kwalla
"eh, ita grandma dinshi ce, i think itama tanada ikon jin abinda ke faruwa tunda itama makusanciyarshi ce" inji daddy
"ba damuwa, muje office din" inji Dr din yana yin gaba
Juyawa daddy yayi ga zee datake tsane idanunta da farin hankin hannunta yayi cupping din fuskarta
"dear, bari muje uhm? Kijiramu anan ok?" yafada a tausashe
Ahankali ta Kada kai, kiss ya mannamata a goshi sannan ya nemi wani acikin maxan yazo shima, nan mallam Nasiru yazo suka wuce tare, ita kau kaka tuni tayi gaba
Binsu da kallo zee tayi har suka shige sannan ta maida kallonta kan kofar dakin da Deen din yake ta kafeta da ido, jitake kamar taje ta bude tashige ta ganshi ko zataji sanyi sanyi a ranta
Komawa tayi ta zauna ta jingina da jikin kujerar tareda lumshe gajiyayun idanunta tana jiran fitowarsu daddy
*OFFICE*
Tunda Dr yafara bayyani kaka keta kuka harya kai aya
"innalillahi waina ilaihi rajiun, innalillahi waina ilaihi rajiun. Dama haka wancan Likitan na Janaral (General) yace, sosai ya gargademu akan kar ya shiga ruwa, ko iska ake sosai yace karya sake yafita babu kayan sanyi, yanzu idan Kamal yatafi yabarni ya zanyi? Ya zanyi da rayuwata ni Ma'u?" taqara Fashewa da kuka tana rufe fuska da gefen zane
"Hajiya kiyi hqr, insha Allah Allah zai tashi kafadunshi, insha allah zai samu lafiya" inji Daddy cikin sigar rarrashi
Dan kallonshi tayi ta gefen ido ta kauda kai tana cewa
"ai dama haka za'ace, dama ai wanda aka cuta ake ba haquri, yaro besan hawaba besan sauka ba anjamashi jinya, yaron daba ruwanshi da kowa, harkar gabanshi kawai yake yanzu gashi anjamashi shiga halin rai ko mutuwa, wannan abu da me yayi kama?" saikuma taqara Fashewa da wani kukan
Kasa cewa komai daddy yayi sai mallam Nasiru dayayi saurin cewa
"haba kaka? Komai fa muqaddarine daga allah, Duk abinda kike ganin yafaru da mutum to allah yariga da ya qaddara Hakan zai faru dashi don Allah kiyi hqr insha allah Deen dinmu zai tashi akan kafafunshi nan kusa"
Bata sake cewa komai ba sai kukan data cigaba dayi
"yanzu Dr zamu iya ganinshi?" inji mallam Nasiru
"A'a Gaskiya don a halin Yanzu baya buqatar hayaniya ko kadan.."
"Dan Allah likita kubari naganshi, wlh bazanyi hayaniya ba, yadda na shiga haka zan fito ko kwakwarar motsi bazanyi ba, Don Allah" inji kaka cikin muryar kuka
"kaka bawai hanaki nayi ganinshi ba, wlh dokace idan mutum na a wannan condition din ba'a barin ashiga dakin, kiyi hqr" inji Dr
"Nidai Don Allah kayi hqr inganshi, bakasan yadda nakeji a zuciyata bane da kasani daka bari na ganshi, don Allah Alhaji kacemashi yabarni na ganshi, shine kadai sanyin idanuna, sanin halin dayake ciki zaisani jin sauqin abinda nakeji a raina, don Allah" tafada tana kallon daddy pleadingly
Kallon Dr daddy yayi yace
"Dr please do something, abarta ta ganshi ko daga nesa ne"
Shiru Dr din yayi na wani lokaci cikin nazari sannan yace
"ok, Gaskiya Saidai ta cctv don it's a strict law patients dake cikin irin wannan condition din babu mai shiga wajensu sai likitoci, wannan dokace akowanne hospital ba a wannan kadai ba
Amma tunda ta nace zamu kaita recording room saita ganshi ta cctv, wannan shine iya taimakon dazamu iya yimata Gaskiya"
"eh babu komai, akaini rekodin din, naji akaini" tafada tana share hawayenta da ha6ar zane
Tashi Dr din yayi yace
"to bismillah"
Duk tashi suma sukayi Dr yayi gaba suka maramashi baya
Jin tafiyar su yasa zee bude idanunta ta dago tana kallonsu
Ganin zasu nufi wata hanyar yasata saurin tashi ta nufo daddy
Ba musu ya miqamata hannu ta kama suka cigaba da bin Dr
Recording room din suka shiga inda duk zirga zirgan da akeyi a hospital din ana ganinshi a wani qaton majigi
Dr din ne yayi ma mutumin dake in charge of wajen magana akan ayimasu zooming din room 12
Yadda yace din haka mutumin yayi, yayi zooming din abinda ke faruwa a dakin da Deen ke kwance
Gasping both kaka da zee sukayi suna rufe baki cikin tashin hankali
Deen ne kwance kan gado sanye da blue kayan asibiti da akewasa marassa lfy
Kanshi nannade da bandage, hancinshi sanye da abin oxygen dake taimakawa wajen jawo numfashi sai hannunshi dakeda cannula anamashi qarin ruwa
Zamewa kaka tayi zata fadi zaune mallam Nasiru yayi saurin kamata ya zaunar daita kan wata kujera
Kafe Deen din cikin majigin tayi da kallo idanunta na tsiyayar hawaye, ganinshi a wannan condition din ba qaramin ta6amata zuciya yayi ba hakan yasa tashiga yin kuka kamar zata shide
Zee kau Fadawa jikin daddy tayi ta rintse idanunta gamm
Bazata iya jurar kallon Deen a wannan halin ba hakan yasa taqara rintse idanunta gamm tana shesheka
Shafa bayanta daddy keyi cikin sigar rarrashi idanunshi na kan Deen din cikin majigi
Dole duk mai imani idan yaga Deen a halin dayake aciki ya tausayamashi
"Dr please do everything you can to save him, please" inji daddy
"insha allah sir, ku kwantar da hankalinku insha allah zai tashi zai koma kamar be ta6a kwanciyaba insha allah" inji Dr din cikin son qarfafa musu gwiwa
Dakyar aka samu aka rarrashi kaka tareda yimata nasihohi sannan suka fito
Alhaji ne yabiya duka bill din treatment din Deen din
Saida suka qara tattaunawa da Dr inda aka fadama kingin yan unguwansu Deen dake wajen halin da ake ciki, sosai kowa ya jajjanta tareda yimashi addu'ar samun sauqi
Nan mazan duk suka tafi da tabbacin zasu dawo anjima da marece aka bar kaka da matar Nasiru da baaba abu sai daddy da zee
Basu dade da tafiya ba motar gidansu zee tashigo hospital din
Wata dattijuwa cikin ma'aikatan gidansu zee ta tafito ita da bala driver daya kawota
Hannunta dauke da basket din abinci wanda mummy tasa akawo musu
Saida suka gagaisa da kowa sunamasu ya jiki sannan daddy da zee suka tashi akan zasubi bala ya ajiyesu gida, ita kuma dattijuwar mai aikin saita tsaya dasu
Godiya su matar mallam Nasiru da baaba abu suka shiga yimashi saboda sosai ya nuna hallaci duba da yadda ya tsaya akansu sosai batareda yayi la'akari da matsayinshi ba na babban mutum
Itakau kaka batama san da tafiyarsu ba don tunda tadawo ta zauna ta buga tagumi ba tace komaiba sai Kafe waje guda da ido datayi
Bayan tafiyarsu daddy ne dattijuwar yar aikin mai suna Inna Binta ta gabatar masu abincin datazo dashi, duk sunci sai kaka da sukayi juyin duniyar akan taci amma taqiya haka suka haqura suka kyaleta
A bangaren zee kau koda suka isa gida mummy ce ta tisata gaba tayi wanka da ruwan masu dumi sosai ta gaggasa jikinta sannan ta tilasta mata taci abinci dukda bada wani yawa taciba sannan tabata maggugunanta tasha tasata ta kwanta
Ko minti biyar ba'ayiba da kwanciyarta barcin gajiya ya saceta
Tasha barci sosai wanda ke cike da mafarkan Deen kala2 wanda tana tashi duk ta mance mafi yawa a cikinsu
Sosai taji dadin jikinta yanzu duk wata gajiya ta tafi sai dan abinda ba'a rasaba saikuma murar datake fama daita haryanzu
Miqewa tayi tashiga toilet ta dauro alwalla sannan tazo ta gabatar da zuhr daya wuceta ta dora da asr da ake cikin lokacinta yanzu
Ta dade tana yima Deen addu'ar samun lafiya sannan ta nemi sakayyar allah akansu nurr dasuka ci amanarta da su master dasuka nufeta da sharri
Saida tagama sannan takoma kan gado ta zauna ta lula duniyar tunani
Ahaka wata maid tashigo kiranta inji mummy
Tashi tayi bayan ta yafa veil din gown dinta ta bita
Kamar yadda ta hasaso abinci mummy zata sata ci
Saida ta gaidata mummy ta amsa tana mata ya jiki ta amsa da da sauki sannan mummy ta zubamata farfesun kan rago wanda yaji kayan yaji sosai ta turamata a gabanta
Babu musu tashiga sha don itama tana buqatar abinda zai dan warware mata toshewar hanci datake fama dashi sai gashi kuma ya taimaka sosai don taji dadin jikinta bayan tasha
Haka taita kasa kunne taji ance ta taso su koma asibiti amma shiru
Gashi batada waya yanzu bare takira daddy ta narkemashi yasa akaita gakuma batason ta tambayi mummy, haka taita jira amma shiru
Daga baya ma saita daure taje tasamu mummyn da maganar sai cemata tayi ba yanzu ba
Abin ya 6ata mata rai sosai Hakan yasa takoma daki ta kulle taita kuka
Sai bayan isha'i mummy ta aika agayamata ta shirya suwuce hospital din
Tuni ta mance da zuciyar datake tayi saurin chanzawa tana addu'ar allah yasa su tararda ya farka
Da ita da mummy dawata maid dinsu suka tafi wannan karon ma da abinci a basket
A asibitin taga daddy Hakan yasa tawuce wajenshi da sauri ta Rungumeshi tana tura baki
Dagota dadi yayi yajamata hanci yana tsokanarta yana kiranta cry cry baby ita kuma sai qara zunbura baki take
Binsu mummy dasukayi gaba suma sukayi suka shiga dakin dasu kaka suke
Saida su mummy suka gama gaisawa dasu kaka sannan itama zee ta gaidata cikin jin kunya kuma ba kunyar komai bace saina tasan tanamata kallon itace silar rashin lfyar jikanta
Amsawa kaka da yanzu ta dan kwantar da hankalinta tayi tana tambayar ta ya jikinta, Amsawa tayi da dasauqi sannan itama ta tambayi lafiyar mai jiki itama ta amsa da dasauqi daga nan kowa yayi shiru
Mummy ce ta gabatar musu da abinci, amsa sukayi suna godiya suka ajiye ko don anjima don basu dade dacin abincin da matar mallam Nasiru takoma gida tayi musuba
Sosai mummy tasaki jiki dasu sukaita fira kamar dama sunsan juna, yadda mummy tasaki fuska tanata fara'a yasa suma suka saki jiki daita sunata hira harda kaka dake tofa nata akai akai
Zee kau tun bayan gaisuwarnan bata qara cewa komai ba saima sadda kai datayi tana wasa da zoben hannunta tana sauraronsu
Hankalinta gabadaya baya tareda su kawai dai tana wajen ne amma ko wuqa za'asa mata bazata iya recalling kalma daya a abinda suke cewa ba
Hankalinta gabadaya na kan Deen, idan akwai abinda tafiso yanzu to sanyashi a ido ne
Sun dan jima a Hakan sannan tadan dago taga haryanzu firarsu suke hankali kwanta
Dan Hadiye yawun bakinta tayi sannan tayi gyarar murya wanda Hakan yasa duk suka kallota, sai kuma taji ta takura da kallon amma saita basar tace
"zan dan je wajen daddy" tafada tana qirqirar wani busashen murmushi
Da to saita dawo su baaba abu suka amsamata suna kallonta yayinda mummy batace komai ba sai kauda kai datayi
Tashi tayi tana dan satar kallon mummy sannan tanufi hanyar fita ta fice
Duk binta da kallo sukayi harta fice sannan baaba abu tayi fuska kalar tausayi tace
"baiwar Allah, kai allah ka cigaba da karemu da zuri'armu wannan abu da me yayi kama? Yarinya nitsatsa amma anason wargazamata rayuwa, allah kacigaba dayimana katangar tsari da ire iren wadannan azzaluman bayin naka"
Duk da amin aka amsa banda mummy da tadanyi murmushi kawai
Wai nitsatsa, Yarinyar da shegen rawar kai yayima yawa wataqila garin Hakan taje ta tsokano ma kanta su don ita haryanzu bata yarda haka kawai zasu nemi wargazamata rayuwa ba
Nan akalar hirar tasu takoma kansu, inda suketa addu'ar tonuwar asirin su master da kuma yin allah wadai dasu sumee dakuma fatan waraka wa Deen
*ZEE*
Ajiyar zuciya ta sauke bayan tafito tana dan juya manyan idanunta
Wawaigawa tayi don ganin inda zata hango su daddyn amma bata gansu ba
Har tayi hanyar office din Dr dinsu saikuma tafasa
Dawowa tayi ta nufi recording room dasuka shiga dazun dasafe
Saida tayi knocking sau hudu sannan aka bude kofar mutumin wata mata ta bayyana
Dan murmushi matar tayimata tace "hi"
Itama maida mata murmushin tayi tace
"hy"
"how may I help you miss?" inji matar tana kallonta
Rasa abinda zatace tayi Hakan yasata fara kame2
Ganin Hakan yasata cewa tashigo ciki sai suyi maganar
Shiga zee tayi tana wondering ina wancan mutumin yake na dazun?
Saida ta zauna sannan matar tace
"yes miss? How may I help you?" inji matar tana folding hannunta tana kallonta
Taking deep breath tayi sannan tace
"amm.. Dama sonake ayiman viewing wani dake kwance a room 12 ne please, patient ne amma anhana shiga ganinshi shine nakeso please kiyimin viewing dinshi"
Shiru matar tayi tana kallonta na dan wani lokaci sannan tace
"am sorry, amma ba'a zuwa ganin mutum anan, kiyi hqr kijira har abaku izinin shiga ku ganshi Hakan ma zaifi"
Shiru zee tadanyi tana kallon zoben hannunta sannan tasake dagowa ga matar
"please, kawai ganinshi zanyi koda flashing dinshi zakiyimin nadan ganshi ki kashe, I want to know how he is please" tafada pleadingly
"idan kinason sanin yadda yake likitanshi zakije ki nema ba nan ba, am sorry but it's strictly against the law, da ana yin haka da kowa ma nan zaizo don ganin nashi, kiyi hqr please ki jira har lokacin da za'a baku izinin shiga ganinshi, am sorry"
Kada kai zee tayi a sanyaye tana qoqarin maida hawayenta sannan ta miqe tsaye
"thank you" tafada ta nufi kofa
Binta da kallo matar tayi har Saida tadora hannu akan handle zata murda
"wane ward yake?" zee ta tsinkayi muryar matar
Juyowa zee tayi da sauri kamar dama jira take tace
"12... Ward 12"
Murmushi matar tayi tace
"ok zo kiganshi na seconds biyar kiwuce kafin azo akamamu anan babu ruwana" tafada tana operating din mouse din hannunta
Da sauri zee tadawo ta zauna tana murmushin jindadi dabatasan tanayiba
Kunnomata matar tayi tayi mata zooming dinshi sannan ta kaucemata don tagani
Tsayawa zee tayi tana kallonshi
Kwance yake kamar dazu haryanzu abin oxygen a hancinshi Saidai yanzu babu qarin ruwa a hannunshi da alamu an cire
"Don.. Allah ma, kidanyimin zooming face dinshi" tafada cikin sanyayar murya
Murmushi matar tayi tayi yadda tace, nan take fuskar Deen yafito daro2 a screen din majigin
Kafeshi tayi da idanu tanajin zuciyarta na kumbura don shauqi
Dukda abin oxygen din ya kare kaso mai yawa na fuskar Hakan be hanata ganin yanda fuskar tayi fayau ba
Idanunshi a lumshe sai lashes dinshi dasukayi zara zara suka hade dajuna sanadiyar lumshe idanun dayayi, ga girarenshi masu cika da baqi dasuka kusan hadewa
Maida kallonta tayi akan ciwon dake akanshi wanda aka nannade da banda sannan akan tulin lallausan sumarshi dake tuje as usual
Kafeshi da idanu tayi bako kyaftawa tanajin kamar zai bude idanu at any moment
Batasan iya lokacin data dauka a haka ba sai jitayi an dafa kafadarta hakan yadawo da ita