Showing 9001 words to 12000 words out of 18571 words
Chapter 4 - Shimfidar Mijina Hausa Novel By Princess Eshat Aysm.txt
a wajen Anwar, takance Fateema ce abun sanyawa Albarka tunda ita tashigo gidan da kyakkyawar niyya, shi kuma yakance duk kyawun niyyan ta idan baki karɓeta ba baza'ayi zaman lafiya ba.
Fateema takanje ta wuni wa Hajiya Jamila, gata kam tana gani tun lokacin datayi aikin da tasa ta.
Maryam kam ta gyara shimfiɗar ta sosai har tafi Fateema k'warewa saboda dama tafi ta kyaw nesa ba kusa ba.
.
.
Yau ta kama Lahadi tun safe Maryam ta tashi da wani irin mura me zafi, har yafara saka mata zazzaɓi, ga tare daya sauk'ar mata lokaci guda.
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
.
.
*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
PML
_We dont just entertain and educate we also touch the hearts of the readears_
.
.
.
Writen By *Princess Eshat Aysm*
.
.
Page 13
.
.
.
.
*Zahra Bello*
"Very interesting book wlh kin burgeni me book dinnan rubutun ki yazo da salo na daban".
.
.
*Zahra Bello*
"Duk book din dazaa rubuta inde an had a mata biyu to se ansa ana rigima da bin boka Amman wannan ya banbanta. Keep it up".
.
.
*Ameenah Ali Musa*
"Gaskiya kika fada zahra, marubuciyar tasauya akalar zamantakewar kishiyoyi d sabon salo, Allah yasa masu kishiya suyi koyi d Maryam D Fatima."
.
.
*Zahra Bello*
"
Gsky akwai fasaha a book din nan".
.
.
.
*Salbiyya Adam*
"Walh nima naji dadinsa sosae allah yasa muna aiki dasakon dake ciki".
.
.
.
.
*Fatima Umar Zubairu*
"Sosai naji dadin da babu boka ba batan hanya, a cikin book dinta, zallan fasaha kawai da dabara takeyi keep it up thanks".
.
.
*Zahra Bello*
".Ai in a zaman aure akwai fahimta to komi yazo da sauki. Fasa da dibara da hskuri sun ishe Mu zaman aure".
.
.
.
*Aliyu Nana Firdausy*
"pls keep it up princess eshat".
.
.
*Zaharaddeen A Ibraheem*
"Very interested book. May almighty Allah (S.W.T) reward u abandontly".
_ire iren wannan cmmnt ɗin ynamun daɗi_
.
.
.
Dayake Anwar yana d'akin Fateema ne baima sani ba, a daddafe ta samu tayi Sallah saboda wani jirin da yake kwasar ta, akan Sallayar bacci ya kwashe ta, sau biyu Fateema tana lek'owa taga tana bacci sai ta koma, don haka tayi aikin ta ita kada'i.
sai kusan k'arfe 10 Anwar yafito, cikin shirin shi da alama futa yakeson yi, d'akin Maryam ya nufa yana tunanin wani irin bacci takeyi har yanzu.
har lokacin bata tashiba, kwanciyar kad'ai ya gani yagani ya fahimci ba kwanciyar jin dad'i bane, kusa da ita ya matsa yad'an rank'wafa kansa zai sumbace ta, da sauri yad'ago jin wani irin hucin zafin daya bugi fuskar shi, hijabin yayi sauri ya warware shi, yana k'ok'arin cirewa ta bud'e idanuwan ta da sukayi ja, ta lumshe su hawaye ya biyo baya saboda wani irin azaban da take ji akan ta, yana wani irin sarawa kamar zai fad'o, a rud'e yafara tambayar ta me yasame ta, ba abunda takeyi sai hawaye, da sauri ya mik'e ya Deb'o ruwa a cup, ya zauna ya mik'e k'afafuwan sa ya jawota yad'aura ta akai, kayan jikinnata ya cire yafara
matsa mata jiki da ruwan, sai da yaji jikin yad'an yi sanyi ya rungumo ta sosai, "me yake damun ki maryam, don Allah kiyi mun magana".
kai kawai ta kad'a mishi, ya dad'a mannata ajikin sa, kafin yayi magana Fateema ta turo d'akin ta shigo, ganinsu a haka sai da k'irjin ta ya buga, da sauri tayi baya zata juya, taji muryan shi yana cewa
"ina zakije"?
bata juyo ba ta k'wak'ulo murmushi ta ce "nazo duba Aunty ne".
ya ce "shine zaki koma"?
bata tsaya bashi amsa ba tasa kai ta futa.
ita kanta maryam kunya taji, daga ita sai pant ajikin ta, gashi ya wani matseta a jikin sa.
Ahankali ya d'agata ya d'auko mata kaya ya sanya mata harda hijabi, sannan yanufi d'akin Fateema, tana jinshi tayi toilet da gudu ta wanke fuskar ta tafito, binta yayi da kallo kafin ya ce "me ya sami idonki"?
murmushi tayi tace k'waro ne yashiga har yanzu ina jinshi, ka huremun, ta isa gaban shi tana ware idanuwan, kama kan yayi, yafara hure wa, yayi sau uku ta ce yafita, sannu yayi mata sannan yace, "zan kai Maryam Asibiti ashe batada lafiya".
tausayi k'arara a fuskanta ta ce "me yake damun ta, shiyasa bata tashiba, sai muje tare".
ya ce "a'a ki zauna yanzu zamu dawo, inaga zazzab'i ne kawai".
Har bakin mota ta rakasu, tanayi wa maryam sannu.
Gwajin farko aka shaida musu cikine ajikin ta, kuka Anwar ya farayi na tsananin murna, a take yayi sujjada yana godiya ga Allah, d'aga Maryam sama yayi yafara juyi da ita, shi kanshi likitan tayashi murna yakeyi, dak'yar ya iya tsayawa aka rubuta musu maganin da zai sa jikin yad'an rage zafi, tsam ya d'auke ta kamar wata jaririya, haka yayi ta ratsawa cikin mutane anata kallon su, bai damu ba don gani yake kamar idan tayi tafiya cikin zai zube.
koda suka isa gida ma d'aukar ta yayi, ta ce "ka sauke ni zan iya tafiya fa".
bai ko saurare ta ba ya tafi abunshi.
Fateema ta k'urawa tv ido taji shigowar su, da hanzari ta mik'e ganin Maryam nad'e a hannun shi, tayi tsammanin ciwon yayi tsanani ne, kawai sai gani tayi Anwar yana danse rawa harda 'yar wak'a
*Soyayya tayi k'arko masoyiy a kula da ita, kada ayi mata ɓatanci sahiba akiyaye ta, Wayyo ni Allah daɗi ya cikani....*
sororo Fateema tayi tana tunanin me zaisa Anwar farinciki haka, haihuwa, tabaiwa kanta amsa, kenan Maryam tasamu ciki, ai batasan lokacin da murna ta kamata ba, itama rik'o maryam tayi tana taya Anwar rawa tana amshi, Maryam daɗi kamar ya kashe ta ganin soyayyar da Fateema take nuna mata, ranar wuni sukayi suna abu ɗaya, duk ciwon da Maryam takeji haka ta daure kada ta ɗaga musu hankali.
Dare ya tsala amma Anwar ya kasa bacci, zuciyar shi sai kitsa mishi takeyi yaje ya dubo maryam, baiyi dogon tunani ba ya mik'e ya nufi k'ofa, Fateema ta ce "ina zakaje".
ya ce "zan dubo baby na".
Dariya tayi ta mik'e tace "muje tare nima inaso mu gana".
ya nok'e kafaɗa ya ce "nak'i wayon".
ta ce "wlh tare zamuje nima nak'i wayon".
da dariyar su suka nufi ɗakin Maryam.
Maryam ta daɗe da bacci saboda maganin da tasha, har rige rigen taɓata sukeyi, a hankali ta buɗe ido, ganin mutane akanta yasa tayi saurin tashi ta zauna tana mutssuka ido, waro ido tayi tace "lafiya"?
Fateema ta ce "yi hak'uri Aunty mun tasheki, rigimane dashi wai zai duba babyn shi".
Maryam ta ce "kodai rigima ne daku, tunda kum tashe ni sai kuzauna muyi ta kallon juna".
Dukkan su suka fashe da dariya, Anwar kamar jira yakeyi yaja hanun Fateema suka zauna a kusa da Maryam, Fateema ta ce "ga shawara, kada mubari Hajiya taga cikinnan, mubata mamaki".
Duk sukay na'am da maganar.
Rayuwa me daɗi sukeyi, Fateema bata gajiyawa ko kaɗan da halin da Anwar yake mata, ranar girkin ta aɗakin Maryam yake kusa kwana wai kada wani abu ya sameta, Maryam tayi2 ya daina yak'i, Fateema tace tabarshi kawai wataran itama zata rama.
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
.
.
*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
PML
_We dont just entertain and educated we also teach the hearts of the readers_
.
.
Writen By *Princess Eshat Aysm*
.
.
Page 14
.
.
_Ina matuk'ar godiya da tarin adduoin da kuke sambaɗo mun Princess har kullum tana alfahari da masoyan ta_
.
.
_Duk wani cmmnt ɗin ku ina gani koda bani nayi postn ba_
.
.
_Ina ganin novel ɗinnan a groups sunfi 30 a fcbk ina godiya sosai_
.
.
.
*MASU CEWA NOVEL D'INNAN YASA SUNJI SUNA SO A MUSU KISHIYA, KUYITA ADDUA ALLAH YA KAWO TA GARI ZAI KAWO*
.
.
*MASOYANA ILYSM💋*
.
.
.
.
Adaidai lokacin Fateema ta cika shekara guda agidan, Maryam kuma tanada shekaru uku, cikin ta wata biyar harya fara fitowa, har lokacin Hajiya batasan Maryam tanada ciki ba, ita bata zuwa gidan ko kaɗan, acewar ta zasu rainata ita kuma akwai son girma, shiyasa batasan abunda yake faruwa ba.
yau tun safe Fateema ta shirya zataje gaishe da Hajiya kamar yadda ta saba takanje mata wuni wani lokaci, a hanya Anwar ya mata siyayya wanda zata kai mata.
Tun shigarsu Fateema taga canji, fuskar Hajiya a murtuk'e, dak'yar ta amsa gaisuwar da suke mata, Fateema ta ce "na shiga uku, kaddai shekara ɗaya har zata dawo kaina....
Maganar Hajiya ne ya katse mata tunani
"Anwar nifa nagaji da irin matar da kake kwasowa, ace har yanzu ba wani labari, to wallahi aure zan maka wacce zata cikamun gida da jikoki, kullum zuwa babu hayaniya babu komai".
Anwar daya zuba mata ido ya ce "Hajiya shifa haihuwa na Allah ne".
Ta taɓe baki ta ce "kullum maganar kenan, Allah yace rashi in taimake ka ai".
Zufa duk yagama wanke Fateema, "nafaɗa mata Maryam nada ciki kawai a huta, kai a'a banyi shawara da Aunty ba".
Ita kaɗai take saka da warwara a zuciyar ta.
Anwar yace "kinga irin wannan rashin hak'urin ne yasa kika so tafka kuskure".
Hajiya ta masa wani kallo kafin tace "yanzu don inaso naga ɗanka shine kake faɗa mun magana, ita waccan saboda taurin kunne kak'i sakin ta, bayan har k'wayoyi takesha, menene kuskure na anan".
Ta k'arashe kamar zatayi kuka, Anwar ya ruɗe ya ce "Ina nufin kuskuren da kikayi na bada magani asawa Maryam, gashi yanzu ta samu rabon ta, Allah ya bata cikinnan".
Zunɓur Hajiya ta mik'e, wani gefen zuciyarta tana nanata Maryam nada ciki, mummunan kallo ta watsa wa Fateema ta ce "Ashe ke algunguma ce? Zuwa kikayi kika faɗa masa? To wallahi bazan zauna dake ki rainani ba".
iya ruɗewa Fateema ta ruɗe, ta kalli Anwar ta fara girgiza mishi kai, shima girgiza mata kai yayi,
"Hajiya me kike tunani ne, ranarda kika bata maganinnan ina tsaye ina gani...
da sauri ta katse shi, "k'arya kakeyi Anwar, yanzu zaka saki yarinyar nan kafin mahaifin ka yadawo k'asar "Hajiya menene laifin Fateema a ciki, don Allah kimun rai kada ki rabani da farinciki na, idan har kika yi haka bakiyi adalci wa kanki...
tsawar data masa shi yasa shi yin shiru, lokaci guda tayi d'aki, da gudu Fateema ta fad'a jikin sa ta saki wani kuka, "kada kabari ta rabamu, ina sonku kaida Aunty Maryam, idan natafi wazai kula...
cikin tsananin tausayi ya had'e bakin shi da nata, biye mishi tayi har suka zauna basu sani ba.
"eyeeeh
*LALATA*
zaku nuna mun? wlh kaji na rantse saika sake ta".
muryar Hajiya suka jiyo, ta futo d'auke da bairo da takadda a hannun ta, a duburbure suka saki juna, Fateema tana kuka ta ce "HAJIYA nayi miki al'kawari bazan rainaki ba...".
ko kallo bata ishe ta ba, cike da masifa ta mik'a masa takaddar, runtse ido yayi ya ce "sai dai kiyi hak'uri, bazan iya saketa babu abunda tamun ba, idan laifine kece me laifi hajiya...".
Kafin ya gama ta tsinke shi da mari har sau biyu, "wlh matuk'ar baka sake ta ba zan tsine maka".
"zan sake ta".
a rud'e Fateema take kallon shi, bai ko kalle ta
ba ya mik'a hanu ya amshi takaddar wajen Hajiya, rubutu yayi ajiki ya nad'e ya baiwa Fateema, Kukan da ta b'oyene ya fito tayi waje da gudu, tana ji yana k'iran ta bata tsaya ba.
wani murmushi yayi ya ce "sai me kike buk'a ta? uwata me ran k'arfe".
Ita kanta jikin ta yayi sanyi, ta shige d'aki ta barshi.
Taxi Fateema ta nema ta nufi gida, sai da ta isa ta d'auko mishi kud'in, taji dad'i ganin Maryam bata falon, idon ta harya kumbura don kuka, bata b'ata lokaci ba ta had'a kayan sawar ta, ta jefa takaddan da Anwar ya bata ajaka, ta sid'ad'a taja kayanta tabar gidan.
Anwar kam gidan Bilal ya nufa suka sha hirar su, kusan wunin sa agidanne baya so ya koma ya tarar da masifar da take tun k'aro shi, a tak'ai ce sai dare ya koma, yasan duk rintsi Fateema bazata sashi kaita Jos a darennan ba.
Maryam yasamu zaune duk kad'aici ya dame ta, tana jiran dawowar su, tana ganin shi ta mik'e ta rungume shi "yau kun cutar dani da yawa, tun safe ni kad'ai".
cikin shagwab'a ta k'arasa, cike da mamaki ya ce "ina Fateemar"?
"Ba tare kuka futa ba? ko kamanta ta agidan Hajiya ne"?
zare hanun shi yayi anata, jiki a sanyaye ya ce "Fateema bata dawo gidannan ba"?
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
Page 15
.
.
*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we also touch the hearts of readers_
_P.M.L_
.
.
writen By *Princess Eshat Aysm*
.
.
*ZARAH MUHAMMAD MAHMUD SURBAJO*
_Ina tayaki murnan kammala KANO TO JIDDAH ina matuk'ar alfari da Novel ɗinki kuma har abada bazan manta dake ba saboda bana manta alkairi, inajin daɗin yanda kika kasan ce baki da girman kai kamar k'anwar ki Eshat, Allah ya daɗa ɗaukaka mun ke, ya shiryar mun dake, ya kuma karemun ke, ILYSM momyn Yusuf_
*muna mungun tare tun kafin mufara writen*
.
.
.
.
A ɗaya daga cikin kujerun Falon ya zauna, yakama kanshi yana jin zafi a ciki, cikin nutsuwa ta isa wajen itama, duk da kujeran ya kasa musu sai da tayi ɗare2 akan cinyar shi, ta tallafo kanshi da hannuwan ta, ta ce "me yake faruwa Husby? A ina kabar Fateema"?
Hanun ta yakama yafara murzawa, a hankali ya shaida mata komai, cikin tashin hankali ta fara masifa, "Nima ba zama zanyi ba, yarinyar da babu ta biyun ta a hak'uri zaka saka? Hajiya ai idan aka mata dabara baza ta gane ba, me yasa zaka....
rufe mata baki yayi ya ce "ki kwantar da hankalin ki Maryam,
Kinsan Hajiya uwata ce, kina so ta tsinemun ne"?
Ta girgiza kai ta ce "a'a".
Yayi murmushi ya ce "yanzu abu ɗaya yaragemun, shine na k'ira naji ko Fateema ta isa garinsu
Nanma gyaɗa masa kai tayi.
Yak'ira yafi a k'irga wayar swchoff, har wani zufa ya farayi, duk k'ok'arin shi kada Maryam taga tashin hankali a tare dashi amma abun ya faskara, itadai sai binshi da kallo takeyi, tunawa yayi yanada numban Sakina, nan yafara k'ira, da yaji numbn ta shiga saida yayi ajiyar zuciya, tare da Sallama ta ɗaga, ta ce "yanzu nake shirin k'iran ka kuwa, sai naga k'awata a gida, kuma sai kuka takeyi tak'i magana, wani abu ya farune?"
Ji yayi hankalin shi ya tashi, amma ya daure harda murmushin sa, ya ce "idan kuna tare taimaka ki bata wayar".
Ta ce "To".
Ko kallon ta Fateema batayi ba, duk nacin Sakeena dole ta hak'ura ta shiga baiwa Anwar hak'uri.
Ya ce "kin gane Sakeena, akwai matsala ne, ki tayani bata hak'uri, ki rarrashe ta don Allah, bana so nasake jin tana kuka, idan ta huce zan k'ira ta".
D'uf ya ka'tse k'iran, mik'ewa Maryam tayi batace komai ba, tausayin Fateema duk ya cikata, abinci ta ɗauko masa ta shirya masa a wajen, bayajin ci ko kaɗan, tabbas yarinyar ta tafi da wani ɓangare nasa, amma duk k'ok'arin da zaiyi ganin Maryam bata gane ba zaiyi, baya so ta fara wani tunani mara tushe da har zai taɓa mata zuciya da abunda yake cikin ta, amma sosai yakejin kewar Fateema a tare dashi.
Bai ankara ba sai ji yayi ta kai abinci bakin shi, bashi da wani zaɓi daya wuce yaci, kamar magani yayi ta ɗurawa har tagama bashi ya cinye tas, kunun ayar ta tsiyaya mishi, nanma ya shanye tas,
Mamaki takeyi irin abincin daya ɗura yau baiyi k'orafi ba, batasan shi baima san yak'oshi ko bai k'oshi ba, murmushi tayi ta ce "kana lafiya kuwa baby"?
Ya zuba mata ido ya ce "me kika gani"?
"naga cinka yayi yawa ne".
Ya lakuce mata hanci ya ce "ke kika ɗuramun".
Ta ce "yau kuma harda sharri? Idan ka k'oshi ai baka bari a ɗura ka".
Yayi dariya ya ce "muje muyi wanka bacci nake ji sosai".
Harda 'yar hamman sa.
Suna fitowa daga wanka ta zura doguwar riga ta fara sallah, ganin haka yasa ya nufi ɗakin shi, kasa taɓuka komai yayi, yarinyar nan akwai shiga rai, yafaɗa gami da tsaki, mik'ewa yayi ya nufi ɗakin ta, anan yagane ta kwashe kayan ta, yayi mamaki da har ta shigo ta kwashi kaya Maryam bata sani ba, k'amshin ɗakinne ya sauk'ar masa da kasala tareda tsantsar kewar ta, ya kwanta a gadon yana tuno rayuwar su, ji yake kamar dun kai shekara da rabuwa, a haka har bacci yayi awon gaba dashi.
Tana idar da sallah ta tashi tayi ɗakin sa, dubawa tayi har toilet baya ciki, gidan ta shiga dubawa amma wayam babu alamar Anwar, shiru tayi tana nazari, can ta nufi ɗakin Fateema, a mik'e ta ganshi yana sharar baccin sa, ajiyan zuciya tayi ta ce "lallai akwai aiki a gabana, ina cikin gidan amma ya kasa nutsuwa har saida ya shigo ɗakinnan, bata bari ranta ya ɓaci ba ta fara tunanin menene mafita, dole ta mantar dashi tunda babu amfani, gaban gadon taje tsaya tana k'are masa kallo, haɗaɗɗen matashi dashi, kyau iya kyau Anwar ya wuce misali, "ni nayi sakaci har wata tasamu daman shiga zuciyar haɗaɗɗan mijina".
Murmushi tayi ta koma ɗakin ta, zama tayi tayi kwalliya sosai, gaba ɗaya gidan ya ɗume da wani irin k'amshi, duk turaren da tasan bata amfani dasu sai datayi a ƙlokacin, shigar bacci tayi, Faɗar irin rigar baccin da tasaka ɓata lokacine, ku k'iyas ta da kanku, cikin ta daya ɗan fito kaɗan ya k'arawa shigar kyau, shi kanshi gashin kanta sai da ta bashi hakkin shi domin wani irin k'amshi ne yake tashi a ciki, kwanciyar ta tayi duk da idon ta ya k'ekashe babu alamar bacci, ganin zata fara mummunar tunani ne yasa ta ɗauko wani littafi na adduoi ta fara karantawa.
.
.
Baccin shi yake sha sosai, duk mafarkin Fateema ne ya cika mishi baccin, sai wajen 12 ya farka, da sauri ya mik'e ganin inda yake baccin, fargaba da tsoron kaddai Maryam ta fito neman shi ne yasashi zare ido, yasan dole bazata ji daɗi ba, cikin sanyi ya koma ɗakin ta, a bak'in k'ofa ya tsaya yana k'are mata kallo, tayi masifar rikita shi, ta zama kamar wata 'yar tsana, bata ko nuna tasan ya shigoba, tanajin shi ma baccin k'arya tayi, rufuwa yaje yayi akan ta ya mata runfa yana shinshina ta, cike da shagwaɓa ta buɗe ido tana hararar shi, marairaicewa yayi ya ce "Bacci kikayi kika manta da ɗan saurayin ki ko".
kuka take shirin farawa ya ce "kiyi hak'uri, idan kikayi nima yi zanyi".
yasa hanu a k'asar cibin ta yana shafawa a hankali, ya ce "Babyn mu yak'i ya girma, anya kina bashi kulawa kuwa"?
Cikin zunɓura baki ta ce "wani irin kulawa ake bashi daya wuce kaci abunda kaji kana son ci".
Murmushi ya yi yace "baki canka ba, akwai wata kulawar".
Zare tawul ɗin jikin sa yayi, ya mirgino da ita kanshi, shi ya koma k'asa, binshi tayi da kallo da idanuwan ta da suka k'ank'an ce saboda sha'awar mijin ta dataji yana fizgan ta, a hankali ya raɗa mata "na nuna miki"?
Kasa ce mishi komai