Showing 6001 words to 9000 words out of 10790 words
Chapter 3 - Allon sihiri Par 2 By Abdul'aziz Sani Madakin Gini.txt
jikin
Yarima Lubainu yayi sanyi yace,yake wannan
sarauniya mai daraja,yanzu kina nufin kice bakya
tsoron irin tsananin tashin hankalin dake cikin
wannan tafiya tawa har kike tunanin zaki ci gaba
da
bina har izuwa lokacin da burina zai cika?
Ki tuna fa
cewa yanzu akan mataki na farko muke kawai.A
kalla nan gaba akwai sauran matakai bakwai
zuwa
goma a gabanmu tunda sai mun nemo barin
Allon
Sihiri na biyu dana uku,sannan mu tafi neman
abokan tafiyarmu mutum uku.Yayin da Sarauniya
Akisatul Sauwara taji wannan batu sai tayi
murmushi
tace,ai rai ba abakin komai yake ba indai akwai
biyan bukata,kuma matsoraci har abada bazai
zama
gwani ba.Yayin da Yarima Lubainu yaji wannan
batu
sai ya cika da mamaki gami da wasi wasi.
Abinda ya
bashi mamaki shine aka wane dalili sarauniya
Akisatul Sauwara ta siyar da rayuwarta don ganin
bukatarsa ta biya?
Abinda zuciyarsa keyi masa wasi
wasi kuwa shine,anya kuwa sarauniya Akisatul
Sauwara bata da wata manufa ta binsa wannan
tafiya?.
A zahiri dai bai ga wani abu dazata amfana
dashi ba kuma bata gaya masa da bakinta
ba.Nan
dai Yarima Lubainu ya taimakawa Sarauniya
Akisatul
Sauwara suka karasa kafa tantin kuma ya
kwance
jakartaya debo kayan shimfidarta ya gyara mata
inda zata kwana.Bayan ya gama kintsa komai a
daidai lokacin da magriba ta kunno kai sai suka
fara
jiyo kukan dabbobin daji dana manyan tsuntsaye
masu shawagi a sama.Koda jin haka sai
Sarauniya
Akisatul Sauwara ta fito daga cikin tantin da
sauri ta
tofa wadansu dalasiman tsafi gabas da
yamma,kudu
da arewa da kuma sama da kasa,sanna ta dawo
cikin tantin ta dubi Yarima Lubainu wanda ke
shirin
biyota izuwa wajen tantin don tabbatar da cewar
babu wani mugun kwaro ko raminsa.Cikin
mamaki
Lubainu ya dubi Akisatul Sauwara yace,mene ne
naga kin fita da sauri daga cikin tantin nan kuma
kin
dawo da sauri?Koda jin wannan tambya sai
Sarauniya Akisatul Sauwara tayi murmushi tace
naje
na samar mana da tsaro ne a waje.Ko dabba ko
mutum ko aljan bai isa yazo nan ba ya cutar da
mu,don haka ka saki jikinka kayi barci mai
dadi.Koda gama fadin haka sai Sarauniya
Akisatul
Sauwara ta nufi inda shimfidarta take ta fara
kokarin
cire tufafin jikinta domin tasa rigar bacci.Cikin
hanzari Yarima Lubainu ya juya ya fice daga
cikin
dakin.Da yake a wannan lokaci wata irin iska mai
sanyi ta fara kadawa,sai Yarima Lubainu yaje ya
samo itatuwa ya kunna wuta ya zauna a gaban
wutar yana jin dumi.A daidai wannan lokaci ne
yaji
yunwa ta kamashi.Don haka sai ya bude jakar
guzurinsa ya fiddo da abinci ya kama
ci.Kwatsam!ba
zato ba tsammani sai yaji takun sawu a
bayansa.Cikin zafin nama Lubainu ya zare
takobinsa
ya mike tsaye zumbur!Koda yai arba da abinda
ya
tunkaroshi sai yai sauri ya sunkui da kansa kas a
lokacin da jikinsa ya kama tsuma.Ba wani abu ya
gani ba face sarauniya Akisatul Sauwara sanye
da
wata doguwar Rigar fara mai shara shara wacce
ta
bayyana komai na surar jikinta.Ganin tsananin
kyawun surar jikin nata ne yasa jikinsa ya kama
kyarma kuma zuciyarsa ta kama bugawa da sauri
da
sauri kuma da karfi.Tunda Yarima Lubainu ya
taso a
rayuwarsa bai taba ganin 'ya mace haka ba a
rayuwarsa sai wannan karon,don haka sai ya
danne
zuciyarsa da karfin tsiya,duk da cewa bashi da
cikakkiyar lafiyar da zaiji
wani abu sai zuciyarsa ta rinka harbawa.Ita kuwa
sarauniya Akisatul Sauwara tazo masa ne a cikin
wannan siffa don ta jarraba iyakar hakurinsa duk
da
cewar shine mutum na farko da ya taba ganinta
a
hakan.Kai tsaye ta matso daf dashi ta dubeshi
cikin
murmushi mai rikirkita kwakwalwa da hankali
tace,shin na baka tsoro ne bisa jin sautin tafiya
ta?
Ba tare da ya dago kai ba ya dubeta sai yayi
yake
sannan yace,ai dole ne naji tsoro tunda ban taba
zaton zanji wani motsi ba a baya.Koda jin haka
sai
Ta bushe da dariya sannan ta kama hannunsa
suka
zauna tare a gaban wutar suka ci gaba dajin
dumin
tare.Koda Lubainu yaga taki sakin hannunsa sai
ya
mike tsaye yace ina zuwa.Kawai sai ya zagaya
bayan tantin yayi kamar yana bawali ne sannan
ya
dawo ya sake zama a kusa da ita suna fuskantar
gabas,amma wannan lokaci bai yarda sun zauna
daf
da daf ba sai daya zamana cewa akwai tazarar
taku
uku a tsakaninsu.Tsawon 'yan dakiku dayansu bai
ce uffan ba sannan Lubainu yayi ajiyar numfashi
ya
dubeta yace,ranki ya dade ya kamata kije ki
kwanta
kiyi barci tunda dare ya soma kuma akwai gajiyar
tafiya a tare dake.Wai shin ma mene ne dalilin
dayasa kika fito ne alhalin gashi kinyi shirin
bacci?
Lokacin da Akisatul Sauwara taji wannan
tambaya
sai tayi murmushi tace,ya kai Lubainu kayi sani
cewa a rayuwata tun daga kuruciyata har izuwa
girmana ban taba kwanciya ba ni kadai a cikin
turakata face tare da kuyangina.Yau gashi zan
kwana ni kadai a cikin tanti kuma a cikin
daji.Tabbas
ko na kwanta barci ba zai zo min ba face ina jin
numfashin dan Adam a kusa da ni.Bisa wannan
dalili
ne na kasa barci har na fito wajenKa.Abinda
nake so
dakai yanzu shine kazo mu koma cikin tantin nan
mu kwana muyi barci.Koda jin wannan batu sai
Idanun Yarima Lubainu suka zazzaro ya dubeta
cikin
alamun tsananin firgici da tsoro yace gaskiya
bazan
iya barci ba a kusa dake.Ranki ya dade kiyi sani
cewa babu wani 'da namiji dazai ganki a cikin
wannan yanayi bai rude ba ya kamu da
sha'awarki
da sonki.Ni a matsayina da saurayin da bai taba
sanin 'ya mace ba kuma wanda yake nisantarku
dole
ne naji tsoron taraiya dake.Koda Lubainu yazo
nan a
zancensa sai Sarauniya Akisatul Sauwara ta
kyalkyale da dariya sannan tace,kamar yadda
baka
taba sanin 'ya mace ba nima ban taba sanin wani
'da namiji ba,don haka na baka amanar kaina.Ina
mai tuna maka cewa samun yin barcina yana
gareka.Koda gama fadin hakan sai Sarauniya
Akisatul Sauwara ta mike tsaye ta shige cikin
tantin
taje ta kwanta akan shimfidarta kanta na kallon
saman tantin ta fada kogin tunani.Shi kuwa
Yarima
Lubainu dake a zaune a wajen gaban wuta sai ya
mike tsaye ya kama kai kawo cikin tsananin
damuwa da wasi wasi.Daga can sai ya shiga
cikin
tantin yayi shimfida a gefe daya nesa da ina
Akisatul
Sauwara ke kwance ya kwanta.
Yana kwanciya sai
zuciyarsa ta tafi izuwa tunanin irin
gwagwarmayar
dayayi a baya.Yana cikin wannan tunani ne kuwa
barci ya saceshi har yana munshari bai sani
ba,kuma bai sake farkawa ba saida gari ya waye
rana ta kwalle.Yarima Lubainu na bude idanunsa
sai
ya hango shimfidar Sarauniya Akisatul Sauwara
wayam babu kowa akai.Koda yayi arba da abinda
ke
kan shimfidar sai zuciyarsa ta buda da kafi ya
kamu
da tsananin mamaki.Ba wani abu ya gani ba
akan
shimfidar face Allon Sihirin nan na Sarauniya
Akisatul Sauwara.Allon ne tsurarsa akan
shimfidar
wato an cireshi daga cikin kwalbar data
lullubeshi.Har Yarima Lubainu ya yunkura zaije
ya
dauki Allon Sihirin sai wata zuciyar ta daka masa
tsawa tace,shin ka manta ne da guzurin da
mahaifinka ya baka kafin ka baro gida.Cin amana
ne
idan ka dauki wannan Allon Sihiri,Amana,cika
alkawari da fadin gaskiya sune guzurin da
mahaifinka ya baka,kuma idan har ka koyayesu
zaka
sami nasarar abinda ka fito nema.Koda gama
aiyana
hakan sai ya juya ya fice daga cikin tantin.Yana
fitowa ya dubi gabasa da yamma,kudu da arewa
amma bai hango Akisatul Sauwara na kuma baiji
motsin taba.Al'amarin d yayi matukar bashi
mamaki
kenan domin baiga dalilin dazai sa tayi
gangancin
barin Allon Sihirin ta ba a fili haka.Nan dai
Yarima
Lubainu ya nufi gabar wannan korama yaje ya
wanke
fuskarsa ya kuskure bakinsa.Ashe duk wannan
abu
dake faruwa Sarauniya Akisatul Sauwara na labe
a
cikin wata duhuwa kuma tana kallon duk abinda
Yarima Lubainu keyi.Ta buya ne domin ta jarraba
amanarsa ta gani shin zai iya rike amanar.A jiya
da
daddare ta jarraba hakurinsa kuma ya haye
jarrabar
tunda har gari ya waye bai kusanceta ba duk da
cewa ya dimauce da ganin tsananin kyawun
siffarta
kuma ya kamu da matukar sha'awarta.Bisa
mamaki
sai sarauniya Akisatul Sauwara taga cewar
Yarima
Lubainu bai dauke Allonta na sihiri ba yayi
kokarin
guduwa.Maimakon hakan ma sai taga cewar
hankalinsa ya tashi bisa rashin ganinta domin
sa'adda ya wanke fuskarsa da bakinsa a cikin
wannan korama sai ya kasa komawa cikin tantin
ya
rinka kai kawo a harabar wajen yana leke leke a
kowacce kusurwa yana kwalla mata kira amma
yaji
bata amsa ba.Al'amarin dayai matukar
dugunzuma
hankalinsa kenan domin yana tsoro kada ya tafi
nemanta kuma azo a sace wannan Allon
Sihirin.Kuma yana tsoron kada ya dauki Allon
Sihirin
zargi ya shiga tsakaninsa da Sarauniya Akisatul
Sauwara.Lokacin da Akisatul Sauwara taga halin
da
Yarima Lubainu ya shiga sai tayi murmushi ta
juya
da baya ta nausa cikin daji.Sai da taje tayi
farauta ta
harbo wani tsuntsu sannan ta dawo.Tana isowa
bakin tantin ta iske shi a zaune yayi tagumi cikin
alamun tsananin damuwa.Koda ya hangota saiya
mike zumbur!da sauri ya tareta yana mai cewa
haba
ranki ya dade yaya zaki tafii cikin daji batare da
kin
sanar daniba.ALLON SIHIRI
Littafi na daya(2)
Part D
Koda ya hangota sai ya mike zumbur!
Da sauri ya
tareta yana mai cewa,haba ranki ya dade,yaa
zaki
tafi cikin daji ba tare da kin sanar dani ba?
Koda jin wannan tambaya sai Sarauniya Akisatul
Sauwara tayi
murmushi tace,komai akwai dalilin faruwarsa.Ka
bari
mu nutsu tukunna zan yi maka bayanin komai a
saukake.
Nan take Akisatul Sauwara ta dora ruwa a
tukunya ta kunna wuta.A takaice dai ta fara
kokarin
fisge wannan tsunstu data harbo.
Koda Lubainu yayi yunkurin taimaka mata sai ta
ki don haka sai
ya
zuba mata idanu har izuwa lokacin data kammala
gasa tsunsun sannan tayi masa tayi suka zauna
suka kama cin nama tsuntsun.
Tsawon yandakiku
suna cin naman dayansu baice uffan ba a lokacin
da
dajin yayi tsit ba a jin sautin komai face na iskar
dake kadawa.
Kawai sai Lubainu ya katse shirun ya
dubeta yace,yake wannan sarauniya mai
daraja,idan
baza ki damu ba inason ki gaya min dalilin
dayasa
kike sakin jiki dani a cikin wannan tafiya alhalin
ban
kasance muharraminki ba ko kuma amintaccenki?
Koda jin wannan batu sai sarauniya Akisatul
Sauwara ta
kyalkyale da daria sannan tace,tabbas
kayi mini tambayoyi masu amfani kuma dama ai
nayi alqawarin baka amsoshinsu a yanzu dana
sami
nutsuwa.
Da farko dai dalilin dayasa na yarda muka
kwana tare a cikin daki ina so ne na jarraba
hakurinka shin zaka kasance mai tsare
mutuncina bisa
alqawarin dake tsakaninmu na taimakon juna a
cikin wannan tafiya?
Tabbas ka kiyaye wannan
jarrabawa ka hayeta.
Dalili na biyu kuma wanda yasa
na tafi na barka a cikin tanti kana barci shine
domin
na jarraba amanarka na gani shin zaka sace
Allon
Sihiri na ne ka gudu?
Sai gashi kayi matukar bani mamaki tunda baka
sace Allon
Sihirin ba alhalin
kuma gashi na fito dashi fili karara daga cikin
kwalbar da babu wani mahaluki daya isa ya fiddo
shi.
Tabbas ka cika mutum mai amana yanzu abu
daya ya rage nayi maka jarraba akansa,kuma da
sannu zamu kai ga wannan matsayi.
Koda Sarauniya Akisatul Sauwara tazo nan a
zancenta sai
Yarima
Lubainu yayi shiru kawai yana mai kura mata
idanu.
Daga can kuma sai ya mike tsaye ya shiga
cikin tantin ya shiga cikin tantin ya shiga hada
kayayyakinsa yana zuba su acikin jakar
guzurinsa.
Itama Sarauniya Akisatul Sauwara ta mike tsaye
ta bishi izuwa
cikin tantin ta shiga
kimtsa na ta kayan.
Har suka gama kimtsa komai
basuce da junansu kala ba.
Nan take suka hau
dawakansu suka nausa cikin daji suna masu
cigaba
da tafiya.Sai da suka shafe sa'a hudu da rabi
suna
tafiya ba tare da sun yada zango ba sannan
Yarima Lubainu ya
matso kusa da Sarauniya Akisatul
Sauwara,da yake dama itace akan gaba tana yi
musu jagora a cikin tafiyar ya dubeta
yace,waishin
tafiyar kwana nawa zamuyi ne mu riski Birnin da
muka nufa?
Koda jin wannan tambaya sai Sarauniya
Akisatul Sauwara tayi murmushi tace,ni kuwa
dadina dakai
kenan ka cika zumudi da gaggawa.
Ai idan
kayi
hakuri idanunka zasu nuna maka.Koda gama
fadin
hakan sai Sarauniya Akisatul Sauwara tayi shiru
bata
kara cewa uffan ba har suka sake shafe sa'a
hudu
suna tafiya.
A sannan ne dare ya riskesu suka yada zango a
bakin wani
katon dutse.
Anan suka kwana
washe gari suka sake yin shiri suka ci gaba da
tafiya.Saida suka shafe kwana bakwai cur basu
riski
wani gari ba kuma basu hadu da wani mugun
abu
ba,kawai dai suna ratsawa ne ta cikin mugayen
dazuzzuka.Duk inda suka hadu da wadansu
mugayen dabbobi
ko kwaruka saidai kaga sun yi
musu kwaf! daya.Kai ko mugayen Aljanu ne suka
hadu dasu saidai kaga Aljanun sun gudu sunyi ta
kansu don sun san cewa WUTSIYAR RAKUMI
TAYI
NESA DA KASA! Kuma RUWA BA SA'AN
KWANDO
BANE.
A ranar kwana na bakwai ne da rana tsaka
Yarima Lubainu ya
hango wani babban gari a
gabansu wanda kawatuwarsa ta ninka ta birnin
Rauhul Bagadar sau uku wato birnin sarauniya
Akisatul Sauwara.Tun daga nesa Yarima Lubainu
ya
wangame baki kamar dan kauye yana kallon gine
ginen birnin cikin al'ajabi.Koda Sarauniya Akisatul
sauwara ta
lura da halin da yake ciki sai ta bushe da
dariya tace,haba ya kai Lubainu kada ka bani
kunya
mana,ai baka ga komai ba ma sai mun shiga
cikin
birnin tukunna.
Koda jin wannan Batu sai Yarima
Lubainu ya sake cika da mamaki yace,waishin
yanzu
kina nufin wannan birnin da zamu shiga shine
Birnin Kimras
inda sarki Darmanu yake mulki inda zamu
samu barin Allon Sihiri na biyu?Akisatul Sauwara
ta
jinjina kai tace kwarai kuwa amma abinda nakeso
dakai shine ka nutsu kada kayi komai da kanka
sai
abinda kaga nayi ko wanda na umarce ka dakayi
saboda Sarki Darmanu ba karamin 2shaidanin
Mutum bane.A
yanzu haka maganar nan da mukeyi nasan
yana kallonmu kuma yana jinmu,kuma zai iya yin
wani abu domin ya cutar damu,don bani da
tabbacin
cewar zai bamu hadin ka bisa bukatar da muka
zo
masa da ita.
Tabbas Sarki Darmanu ya fini karfin
Sihirin tsafi,amma fa a bangaren jarumtaka da
iya yaki KARE
JINI BIRI JINI mukeyi.
Sau tara muna
fafatawa ni dashi ba tare da wani yayi nasara a
tsakaninmu ba amma fa muna matukar jin jiki.
Bisa
sa'a ne kawai na samu na tsira daga sharrin
tsafinsa
saboda tsarin dana samu tun daga
kakannina.
Lokacin da Sarauniya Akisatul Sauwara tazo
daidai nan a
zancenta suna daf da shiga cikin
birnin ne,
Kwatsam!sai suka ga wani mutum Tsoho
tukuf ya fito dafa cikin gona goye da kara a
bayansa,shima zai shiga cikin birnin.Cikin Ladabi
Sarauniya Akisatul Sauwara da Yarima Lubainu
suka
gaishe da tsohon.Kawai sai tsohon ya kare musu
kallo ya lura
cewa baki ne don haka saiya dubesu
yace,yaku wadannann matasa hakika ku baki ne
a
garin nan ko?
Akisatul Sauwara tace,Baba zancenka
dutse ne.Tsohon ya dubi Sarauniya Akisatul
Sauwara cikin yanayi
mai nuna tausayi yace,Yarinya bisa yanayinku da
gani kun fito
daga babban gida kuma kun sami
tarbiya mai kyau,saboda haka zan taimakeku don
kada ku fada cikin tarkon maketacin
sarkinmu.Ina
mai sanar daku cewa bisa al'adar wannan mugun
sarki namu duk bakon daya shigo garin nan
kamashi ake yi a kwace duk abinda ya mallaka a
kaishi
kurkuku a kulle ko kuma ayi masa dukan kawo
wuka sai idan yana da sauran shan ruwa a
duniya
sannan zai tsira da rayuwarsa.
Yanzu zan taimake ku
zna bi daku ta barauniyar hanya inda babu wanda
zai
ganku harmu isa gidana inda zaku kwana,in yaso
indan gari ya
waje sai ku saje da 'yan gari ku
aiwatar da abinda ya kawoku.Tsohon na gama
fadin
hakan kuma sai ya dubi Yarima Lubainu
yace,idan
sarki ya kyallara ido yaga wannan kyakkyawar
'yar
uwar taka saiya rabaka da ita har abada.
Koda jin
haka sai Yarima Lubainu ya gyada kai yana mai
jinjina
al'amarin ba tare da yace kala ba.
Nan dai
tsoho ya wuce gaba suka bishi a baya yana mai
bin
wata barauniyar hanya wacce tabi bayan birnin.
Su kuma suka ci gaba da jan limzamin
dawakansu a
hankali suna yin tafiyar san'da suna waige waige
cikin rashin yarda da kwanciyar hankali.Lokacin
da suka yi 'yar
doguwar tafiya ya zamana cewa tsohon
yana gabansu da tazara ta a kalla taku goma sha
biyar sai Yarima Lubainu ya dubi Sarauniya
Akisatul
Sauwara yayi mata magana cikin karamar murya
yace,nifa ban yarda da wannan tsohon ba,domin
zai
iya zama dan leken asirin Sarki Darmanu ne aka
turoshi ya
yaudare mu ya cutar damu.
Koda jin
wannan batu sai Sarauniya Akisatul Sauwara taji
zuciyarta ta buga da karfin gaske,take tsoro ya
baibayeta kuma taji ta gamsu da tunanin da
Yarima
Lubainu yayi,don haka sai kawai taja linzamin
dokinta ta tsaya cak!shima Yarima Lubainu sai
ya tsaida nasa
dokin suka kurawa tsohon idanu kawai
yayin da yake ci gaba da tafiya.Koda tsohon yaji
sautin sauwun dawakansu Lubainu ya dauke a
bayansa sai shima ya tsaya cak ya juyo da sauri
cikin alamun mamaki ya dubi su Lubainu yace
'ya'yana lafiya kuwa kuka tsaya a baya haka
kuka daina tafiya?
Caraf sai Sarauniya Akisatul Sauwara ta
dubi tsohon ta daka masa tsawa tace,kai tsohon
banza!bakin mayaudari na gane ko kai
waye.Maza
ka bayyana surarka ta gaskiya domin mu
tattauna
bisa abinda ya kawomu birninka.Lokacin da
tsohon
yaji wannan batu na sarauniya Akisatul Sauwara
saiya bushe
da mahaukaciyar dariya cikin karfin
murya mai nuna cewa lallai ba muryarsa bace ta
tsoho.Daga can kuma sai yayi girgiza nan take
ya
rikide ya zama sarki Darmanu cikin gagarumar
shigar yaki.
Sarki Darmanu ya kasance katon mutum
mai kirar sadaukai,gashi dogo zankalele kuma
gashi kakkaura
mai murdadden jiki gami da tarin kwanji
da
jijiyoyi.
KALLO DAYA mutum zai masa ya gane cewar
ya cika sadauki mai TARWATSA MAZA.
Wadansu
bakaken kayan yaki ne a jikinsa na karfe.
Rigar dai
Farmaran ce mai budadden hannu,sai dogon
wando da
dogayen takalma duka na bakin karfe.
A hannunsa na hagu kuwa wata katuwar garkuwa
ce
wadda akayi ta da zallan dutsen lu'u lu'u mai
nauyin
gaske wacce sai kato goma sun taru suke iya
rabata
da kasa amma shi ji yake kamar takarda ya
rike.
Bayan anyi kallon kallon na tsawon dakika goma
tsakanin sarki Darmanu dasu sarauniya Akisatul
Sauwara sai Sarki Darmanu ya sake bushewa da
dariyar mugunta karo na biyu sannan ya dubi
sarauniya Akisatul Sauwara yace,ke tsohuwar
abokiyar gaba kiyi sani cewa tun kafin ku baro
birnin ki naga
duk abinda ya faru tsakaninki da
Yarima Lubainu dan sarki Sailur har izuwa
sa'adda
kuka taho izuwa nan birnina domin na baku barin
Allon Sihirin dake hannuna.
Tabbas dake dashi kuma
sami tabin hankali har da kuke tunanin zan
karbeku
hannun bibbiyu na yarda da bukatarku.
Kisa sani cewa na dade ina jiran irin wannan
rana wacce
zakuyi gangancin dauko barin Allon Sihirinki ki
taho
har izuwa birnina domin tuni nayi bincike na
gano
yadda zan iya fidda Allon daga cikin kwalbar
dakika
adanashi.Kin ga kenan yanzu na sami tsuntsu
daga
sama gasasshe tunda kin kawo kanki.Yanzu zan
hallaku na
dauke Allon Sihirin daga jikinki naje na
biya tawa bukatar dashi.
Koda gama fadin hakan sai
Sarki Darmanu yai wuf ya daka tsalle a sama
kamar
an cilloshi daga cikin baka ya kawowa Akisatul
Sauwara da Lubainu mugun sara a sama da duk
su
biyun a lokaci guda.Cikin bakin zafin nama duk
su biyun suka
kaucewa saran suka fado kasa daga kan
dawakansu,ai kuwa sai takobin sarki Darmanu ta
tsarge dawakan biyu tamkar an yanka tsakiyar
tuffa.
Take dawakan suka zube kasa matattu.Cikin
sauri da dimauta su Lubainu suka mike tsaye
zumbur suna masu zare nasu takubban.Sarauniya
Akisatul
Sauwara tayi sauri ta tofawa takobinta da
takobin Lubainu wani dalasimin tsafi sai
takubban
nasu suka kara kaifi,girma da nauyi.Koda ganin
haka
sai Sarki Darmanu ya rugo da gudu izuwa kansu
suka runtsume da azababben Yaki.
Shegen kaya Uban mayaudara Sarki Darmanu.
6 hrs · PublicALLON SIHIRI
Littafi na biyu(2)
Part E
Sannan su dauke mu mu ci gaba da tunkarar
gidan
Boka Darbusa.Yanzu ga dawakai nan guda biyu
dana
tanadar muku sai ku hau mu kara gaba.Ba tare
da
gardamar komai ba kuwa Lubainu da sarauniya
Akisatul Sauwara suka hau wadannan dawakai
suka
bi bayan Sarki Darmanu suka fice daga cikin
birnin
gaba daya.Nan dai suka nausa cikin daji suka yi
ta
tafiya ba sassauci har suka shafe sa'a goma sha
biyu ba tare da sun hadu da wani mugun abu
ba.Duk wata muguwar dabba idan ta hangosu
daga
nesa sak kaga ta ratsa ta sauya hanya,haka ma
mugayen aljanu.Yan fashi kuwa da zarar sun
hango
Sarki Darmanu tare dasu Lubainu sai kaga sunyi
ta
kansu saboda sun san cewa Bakin Rijiya ba
wajen
wasan yaro bane.Adaidai wannan lokaci ne
magriba
ta riskesu kuma a sannan ne suka shigo farkon
dajin
da wadannan tsuntsaye na sarki Darmanu
suke.Da
shigarsu cikin dajin sai Sarki Darmanu ya daga
kansa sama yana mai karanta wadansu dalasimai
na
tsafi.Faruwar hakan keda wuya sai Lubainu da
Sarauniya Akisatul Sauwara suka ji wata irin iska
mai karfin daga sama ta fara kadawa.Kwatsam
sai ga
wadansu jibga jibgan tsuntsaye guda uku sun
bayyana suna masu saukowa kasa.Duk su ukun a
gaban sarki Darmanu suka sauka suna masu
dukar
da kawunansu alamar cewa sun kwashi
gaisuwa.Nan
take sarki Darmanu ya shafa kawunan wadannan
tsuntsaye yayi magana dasu a cikin yaren
tsafi.Faruwar hakan ke da wuya sai tsuntsayen
suka
bude fukafukansu suka sake tashi sama suka
luluka
a cikin gajimare har suka bace bat tamkar basu
taba
wanzuwa ba.A sannan ne Sarki Darmanu ya dubi
Yarima Lubainu da Sarauniya Akisatul Sauwara
yace,anan zamu yada zango mu dan huta nan da
cikar kamar sa'a uku wadannan tsuntsaye zasu
dawo su daukemu mu ci gaba da tafiya.Nan take
suka kafa tanti suka fidda abincinsu na guzuri
suka
kama ci suna hira.kafin Yarima Lubainu yayi wani
abu da hannunsa tuni Sarauniya Akisatul
Sauwara ta
miko masa,ya zamana cewa tana kyautata
masa,bata son taga ya yi wani abu na wahala da
kansa face ta taimaka masa.Bayan sun gama cin
abincin ne Akisatul Sauwara ya mike tsaye ta
dubesu tace,tana son ta zagaya bayan wata
katuwar
bishiya dake can gabansu tayi bawali.Tana gama
fadin hakan sai ta juya ta nufi inda wannan
bishiyar
take.Tana isa kuwa ta zagaya bayan